Jihar Zamfara
An kashe ‘yan bindiga da dama a wata arangama da aka yi tsakanin ‘yan bindiga da ke gaba da juna a kusa da Mada hanyar Gusau da karamar hukumar Tsafe, jihar Zamfara.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare, ya kai ziyara ta musamman kauyuka biyu da ƴan bindiga suka tafka aika-aikata a kananan hukumomin Zurmi da Birnin Magaji.
Mambobin majalisar dokokin Zamfara sun tsige kakakin majalisar, Bilyaminu Moriki, saboda matsalar tsaro da ta addabi jihar sannan suka maye shi da Bashar Gummi.
Gwamnatin Dauda Lawal ta kawo jami’ai 2, 645 da za su yaki ‘yan bindiga a Zamfara sai aka ji Magaji Lawal ya mutu a hannun Askarawa a wani yanayi mai alamar tambaya.
Kwamishinan 'yan sandan jihar Zamfara, CP Kolo Yusuf, ya bayyana cewa an kammala duk wani shirin shiri domin ganin an kawo karshen ayyukan 'yan bindiga a jihar.
Ana zargin hukumar tsaro ta Community Protection Guard (CPG) a jihar Zamfara da kisan wani dan siyasa, Magaji Lauwali da ta ke zargin ya na da alaka da mahara.
Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun kai mummunan hari a hedikwatar 'yan sanda da ke garin Zurmi na jihar Zamfara. Sun tafka barna sosai.
Wasu miyagun 'yan ta'adda dauke da bindigogi sun kai sabon farmaki a jihar Zamfara inda suka halaka mutum bakwai tare da yin garkuwa da wasu mutum 20.
ʼYan bindiga na cin zarafin matan aure da tsakar rana a wani ƙauye dake karamar hukumar Tsafe da ke Zamfara. Har yanzu maganar ba ta mamaye kafefen yaɗa labarai ba.
Jihar Zamfara
Samu kari