Hukumar Sojin Najeriya
Biyo bayan wani harin bam da rundunar soji ta kai kan wasu masu maulidi a Kaduna, Shugaba Tinubu ya bayar da umurnin yin bincike. Ya kuma jajantawa al'umma.
Femi Fani-Kayode, tsohon ministan sufuri, ya ce DSS sun dakile shirin dakarun soji na yin juyin mulki zamanin Shugaba Muhammadu Buhari. Ya kuma jinjinawa Yusuf Bichi
Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Kaduna, Samuel Aruwan. ya ce hukumar sojin ƙasa ta Najeriya ta ce ita ta yi kuskuren kai harin bam kan yan Maulidi.
Hatsarin jirgin sojin da ya auku a Patakwal, babban birnin jihar Ribas shi ne na hudu da ya faru a shekarar 2023 wada ke shirin karewa nan da wata ɗaya.
Rahoton shelkwarar soji ya nuna cewa dakarun soji sun kashe sama da 'yan ta'adda 180, sun cafke 204 yayin da suka kubutar da mutum 234 da aka yi garkuwa da su.
Wasu mayaƙan ISWAP huɗu sun bakunci lahira yayin da bam ɗin da suna ɗana wa sojoji tarko da shi ya tashi da su ranar Laraba da ta gabata a jihar Borno.
Jami'an tsaro sun samu nasarar kama wata tawagar yan bindiga mai kunshe da mutum takwasa a jihar Kaduna, ana zargi su suka sace sakataren tsare-tsaren APC.
Kungiyar mafarauta ta jihar Taraba ta ankarar da cewa yan bindiga sama da 300 sun zagaye birnin Jalingo, kuma sun kashe mata jami'ai akalla 22 a sassan jihar.
Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umaru Zulum, ya yi kira ga mahukuntar gidan soja da su ƙara girke dakarun sojoji a shiyyar Arewa maso Gabashin Najeriya.
Hukumar Sojin Najeriya
Samu kari