Hukumar yan sandan NAjeriya
Jami'an rundunar 'yan sandan jihar Kano, sun yi arangama da wani hatsabibin dan daba mai suna Baba Beru. 'Yan sandan sun aika da shi barzahu bayan fafatawa.
IGP Kayode Egbetokun ya haramta tura jami'an MOPOL zuwa tsaron manyan mutane. Ya bukaci a janye su daga ayyukan da ba su dace ba domin dawo da martabar rundunar.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Kwara. 'Yambindigan sun bude wuta kan mutane wanda hakan ya yi sanadiyyar rasa rayuka.
Rundunar ‘yan sandan Kaduna ta ce bindigar mafarauta ce ta kashe yaro dan shekara 12 a Abakpa, ba fashewar bam ba. Ana ci gaba da bincike a kan lamarin.
Yayin da sace-sacen al'umma ya yi ƙamari a Edo, Gwamnan Monday Okpebholo, ya dakatar da sarkin Uwano, Dr. George Egabor, bisa yawaitar garkuwa da mutane.
Mai ba gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori shawara ta musamman kan harkokin kasuwanci da safara, Chief Love Shimite ya mutu, ƴan uwa suna zargin mijinta.
Rahotanni sun bayyana cewa zanga zanga ta ɓalle a jihar Filato karkashin CAƁ sakamakon ƙaruwar hare-haren ƴan bindiga a kananan hukumomin Bassa da Bokkos.
Tsohon ministan tsaron Najeriya, Janar Theophilus Danjuma, ya yi kira ga 'yan Najeriya da su tashi tsaye domin kare kansu saboda gwamnati ba za ta iya ba.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kai harin ta'addanci a garin Kware da ke jihar Sokoto. 'Yan bindigan sun kona kasuwar garin tare da raunata mutane masu yawa.
Hukumar yan sandan NAjeriya
Samu kari