Labaran garkuwa da mutane
An samu tsaiko a wata jihar Kudu yayin da wasu 'yan bindiga suka farmaki mambobin jam'iyyar APC a lokacin da suke tsaka da gudanar da taron jam'iyyar a jihar.
Wasu miyagun ‘yan bindiga sun kai farmaki gidan basarake kuma tsohon alkali a cikin Jalingo. Sun yi garkuwa da matansa biyu tare da tasa keyar ‘ya’yansa shida.
Yanzu muke samun mummunan labarin yadda wasu tsagerun 'yan bindiga suka sace daliban makarantar firamaren gwamnati a wata jihar Arewa, jihar Nasarawa a Arewa.
hukumar NSCDC a jihar kaduna ta bayyana bukatar dangi su fito domin maye gurbin jami'anta 7 da aka kashe a wata arangama da tsagerun 'yan bindiga a jiha Kaduna.
Gwamnatin jihar Edo ta sanar da cewa wasu Sarakunan gargajiya guda 2 sun shiga hannu bisa zargin hannu a harin sace fasinjojin jirgin kasa a ranar 7 ga wata.
A ranar Lahadi, 15 ga watan Janairu ne yan bindiga suka kai hari cocin Life For All a karamar hukumar Kankara ta Katsina, inda su ka yi garkuwa da masu bauta.
Rundunar sojin Najeriya ta yi nasarar sheke wasu tsagerun 'yan bindigan da suka addabi jama'a a yankunan jihar Kaduna. An fadi adadin wadanda aka kashe take.
Hukumar 'yan sanda reshen jihar Katsina ta bayyana jerin sunayen mata 5 da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a Kauyen Mai Tsauni, karamar hukumar Kankara.
Wasu 'yan ta'adda sun kai farmaki wata coci da ke Jan Tsauni a karamar hukumar Kankara ta jihar Katsina inda suka tasa keyar mutum 25 tare da raunata fasto.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari