Labaran garkuwa da mutane
Hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta bayyana matsayarta game da yadda take shirin yin zaben 2023. Ta ce bata taba tunanin dage zabe ba, don haka za a yi zabe.
Rundunar yan sandan jihar Katsina a ranar Laraba, 11 ga watan Janairu ta tabbatar da kama wasu matasa uku kan zargin sace yarinya yar shekara shida a Kano.
Wasu miyagun 'yan bindiga sun kutsa yankin Bwari da ke babban birnin tarayya inda suka sheke wani magidanci da suka yi artabu da shi. Sun yi garkuwa da yaransa.
Wasu tsagerun 'yan bindiga sun gamu da matsala yayin da 'yan banga suka kwamushe su a wani yankin jihar Bauchi. An bayyana yadda lamarin ya faru da kuma mataki.
Yan sanda a jihar Plateau sun kama wani fasto mai suna Albarka Sukuya kan garkuwa da kansa har sau biyu yana kuma karbar kudin fansa daga mabiyansa a cocin ECWA
Wasu tsagerun 'yan bindiga sun hallaka wata mata mai juna biyu, inda suka hallaka wasu mutum uku kuma daban duk dai a lokacin da suka kawo farmaki a Anambra.
An yi alkawarin ceto wadanda aka dauke a tashar jirgin kasa a Edo. Kwatsam sai ga shi ‘yan bindigan su na neman a biya kudin fansar N20m a kan duk mutum daya.
Gwamnatin jihar Edo ta tabbatar da ceto wasu mutum shida daga cikin wadanda 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a farmakin filin jirgin kasa da suka kai jihar.
An shiga halin fargaba a Jihar Edo a safiyar ranar Litinin bayan wasu yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun yi garkuwa da wani tsohon dan majalisar jihar.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari