Labaran garkuwa da mutane
Yanzu muke samun labarin yadda wasu 'yan bindiga suka yi bata-kashi da 'yan sanda, inda aka ceto wani dan jairdan da aka sace a makon nan, ranar ta Alhamis.
Rundunar 'yan sanda reshen jihar Zamfara sun lalata wani mafakar yan fashin daji a Zamfara, sun kubutar da mutane 14 da suka shafe sama da watanni biyu a daji.
Wasu tsagerun yan bindiga sun kutsa kai rukunin gidajen Grow homes estate da ke yankin Kubuwa a babban birnin tarayya Abuja, sun yi garkuwa da akalla mazauna 9.
Yan bindiga a Kaduna sun kai hari garuruwan Karimbu-Kahugu a karamar hukumar Lere a Kaduna a safiyar ranar Juma'a inda suka kashe dan fasto tare da sace matarsa
Rundunar yan sandan jihar Zamfara sun yi nasarar kama wani matashi mai suna Thomas Ya'u dan shekara 20 kan zargin garkuwa da mahaifiyarsa ya karbi fansar N30m.
A wani sabon hari da aka kai jihar Kaduna, miyagun 'yan bindiga sun yi garkuwa da matar aure, 'ya'yanta biyu da wasu mazauna 9 a ƙauyen Janjala, yankin Kagarko.
Rundunar yan sandan Bauchi ta ce jami'anta tare da taimakon yan banga sun samu nasarar dakile harin garkuwa da wasu mahara suka kai Rafin Gora, yankin Ningi.
Wasu mahara da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane sun je har gida sun yi awon gaba da iyalan basaraken Sarkin Kudu a jihar Taraba ranar Jumu'a da dadare.
Wani basaraken gargajiya a yankin birnin tarayya Abuja, HRH, Alhaji Hassan Shamdozhi, ya bayyana yadda ake cikin bayan sace matarsa ɗa yayansa kusan wata 1.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari