Labaran garkuwa da mutane
Masu garkuwa da mutane sun sace wani mawaki da masu masa kida a hanyar Abuja zuwa Kogi. Yan bindigar na neman nara miliyan 10 kudin fansar duk mutum daya.
Shugaban jami'ar FUDMA, Farfesa Armaya’u Hamisu-Bichi, ya sanar da cewa ragowar ɗalibai mata hudu da ke hannun yan bindiga sun shaki iskar yanci.
Yan bindiga sun shiga garin Zurmi, hedkwatar ƙaramar hukumar Zurmi a jihar Zamfara, ana fargabar sun sace mutane 10 ciki har da mai jego da jaririnta.
Wasu yan bindiga sun yi awon gaba da mutane 12 a kauyen Gbaupe da ke ƙarƙashin birnin tarayya Abuja ranar Lahadi, sun kuma kashe jami'in yan banga ɗaya.
Wasu tsagerun yan bindiga sun shiga kauyen Unguwar Liman a karamar hukumar Igabi ta jihar Kaduna, sun sace mutane harda mata da kananan yara masu yawa.
An kai hari a Gidan Shaho washegari aka koma kauyen Nasarawar Zurmi inda aka yi asarar mutane, rayuka, dukiya da abinci. Yanzu Mutane sun tsere da suka koma Zamfara
Labari ya zo mara dadi yanzu nan cewa ‘Yan bindiga sun kai hari a unguwar Zone 5 da ke yankin gidajen da ke rukunin Kubwa a birnin tarayya Abuja.
Mr. Samuel Soyemi ne ya ba da labarin yadda wasu jami'an 'yan sanda suka sace shi da iyalinsa tare da karbar Naira miliyan daya da kwashe wasu kayayyaki.
Hukumar Gidajen Yari (NCS) ta yi martani kan jita-jitar cewa an yi yunkurin yin garkuwa da Emefiele karfi da yaji a gidan yarin Kuje da ke birnin Abuja.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari