Karatun Ilimi
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nada Malam Haladu Mohammed Mai Ba da Shawara kan Inganta Ilimi. Wannan nadin na daga cikin matakan gwamnati inganta ilimi.
Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ta amince da kafa sababbin jami'o'i na kudi guda 11, hukumar NUC ta ba su lasisi a Abuja.
Gwamnatin Uba Sani ta Kaduna ta bayyana cewa an kwace wasu filayen makarantu da tsohuwar gwamnatin jihar ta cefanar domin inganta koyo da koyarwa a makarantun.
Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta ce za ta zakulo daliban da suka yi hazaka a jarrabawar JAMB din da ta dauki nauyi, domin a zaba masu wasu manyan makarantu.
Malaman firamaren birnin tarayya Abuja sun shiga yajin aiki karo na hudu, saboda gaza biyansu sabon albashi na N70,000. Lamarin ya hana dalibai zana jarabawa.
Dan Majalisar Tarayya daga jihar Sokoto, Hon. Sani Yakubu ya dauki nauyin karatun wasu dalibai 21 a jami’a domin tallafa musu wajen samun ilimi mai inganci.
Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta bayyana cewa ta kwato kudade mafi yawa a shekarar 2024 daga hannun barayin da suka sace kudin gwamnati.
Gwamnatin jihar Katsina ta fito ta kare matakin da ta dauka na rufe makarantu a lokacin azumin watan Ramadan. Ta bayyana cewa akwai dokar yin hakan.
Gwamnatin Ondo ta ware N634m don biyan kudin WASSCE na 2024/2025 ga dalibai sama da 23,000, da nufin ba 'ya'yan talakawa damar yin karatu ba tare da matsala ba.
Karatun Ilimi
Samu kari