Gwamnatin tarayyar Najeriya
Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ta kaddamar da shirin bai wa matasa rancen kuɗi har N200,000, za a fara da yan NYSC.
SEREC ta ce Najeriya na fuskantar barazanar rasa haraji da zuba jari na N1.6tn saboda durkushewar tashoshin ruwa da rashin ingantattun hanyoyin sufuri.
Gwamnatin tarayya ta yanke hukuncin korar ma'aikatan hukumar gyaran hali ta ƙasa su 15, ta kuma rage wa wasu 59 matsayi saboda aikata laifuka da rashin ɗa'a.
Tsohon ministan kula harkokin ƴan sanda, Aminu Maina Waziri ya ce gwamnatin shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ta maida Najeriya baya ta kowane fanni.
Ministan harkokin Abuja, Mista Nyesom Wike ya bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ba za ta iya warware duka matsaloin ƴan Najeriya ba.
Ministan harkokin Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa mutane irinsa da ke fama da shugabanni masu ganin sun fi karfin doka, suna buƙatar addu'a daga ƴan ƙasa.
Masanin tsaro, Sani Shinkafi ya zargi gwamnatin tarayya da dakile yunkurin kama Bello Turji ko kashe shi a Zamfara duk da cewa CJTF sun kusa gamawa da shi.
Kungiyar kare hakkin musulmin Najeriya watau MURIC ta buƙaci gwamnatin tarayya ta kafa kotunan shari'ar musulunci a kowace jiha a ƙasar nan birnin tarayya.
Tinubu ya sauke Madueke daga shugabancin hukumar NCCC, tare da maye gurbinta da Majekodunmi. An ce sabuwar shugabar na da kwarewar aiki na sama da shekaru 17.
Gwamnatin tarayyar Najeriya
Samu kari