Labari Mai Daɗi: Malaman Makaranta Za Su Samu Ƙarin N35,000 a Albashi Duk Wata a Jihar APC

Labari Mai Daɗi: Malaman Makaranta Za Su Samu Ƙarin N35,000 a Albashi Duk Wata a Jihar APC

  • Gwamnatin jihar Legas ta yi ƙarin haske kan alawus ɗin N35,000 na rage raɗaɗin halin da ake ciki ga malaman makaranta
  • Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya bayyana cewa malaman firamare zasu samu wannan tallafin daidai da yadda ake biyan sauran ma'aikata
  • Sanwo-Olu ya ce malaman makarantun jihar Legas za su samu ƙarin N35,000 a matsayin tallafi kamar yadda ake biyan sauran ma'aikatan gwamnati

Jihar Legas - Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas, ranar Alhamis, 29 ga watan Fabrairu, ya ba da umarnin a cire banbanci wajen biyan tallafin albashi na N35,000.

Gwamnan na jam'iyyar APC ya bada umarnin kada a sake nuna banbanci wajen biyan waɗannan kuɗin rage zafi ga malaman makarantun gwamnati a Legas.

Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas.
Malaman Makaranta Zasu Samu Karin N35,000 a Legas Hoto: Babajide Sanwo-Olu
Asali: Facebook

Idan baku manta ba a watan Disamba, 2023, gwamnan ya amince da biyan N35,000 ga duk ma'aikatan jihar.

Kara karanta wannan

Gwamnan PDP zai ba 'yan adawa mukamai masu gwabi a jiharsa, ya fadi dalili

Wannan ƙarin N35,000 a albashin ma'aikatan an yi shi ne domin rage musu raɗaɗin halin da aka shiga na tsadar rayuwa gabanin a ƙarkare batun sabon mafi ƙarancin albashi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kamar yadda Vanguard ta tattaro, kwamishinan ilimi a matakin farko da na sakandire, Jamiu Alli-Balogun, ne ya bayyana haka a wurin taron masu ruwa da tsaki.

Ali-Bologun ya shaida wa kungiyar malamai (NUT) a ofishinsa cewa Gwamna Sanwo-Olu ya umarci a cire banbancin N20,000 da ake biyan malaman Firamare maimakon N35,000.

NUT ta yabawa Gwamna Sanwo-Olu

Shugabannin NUT karƙashin Kwamared Hassan Akintoye, sun yabawa gwamnan bisa wannan tagomashi da ya kara wa mambobin ƙungiyar.

Sun kuma bayyana cewa wannan matakin zai magance korafe-ƙorafen da malaman makaranta suke yi.

Akintoye, ya yabawa gwamnatin jihar Legas bisa ƙaunar da take yi wa malamai da kuma ci gaban ilimi.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya gamu da cikas a CBN, wanda ya naɗa ya yi watsi da muƙamin kan dalili 1

Shugaban ya kuma jaddada goyon bayansa ga jihar baki daya tare da yin alkawarin "ci gaba da taimakawa gwamnati wajen cimma burinta na inganta koyo da koyarwa a jihar."

Tinubu ya soki ƴan kwadago

A wani rahoton kuma Bola Ahmed Tinubu ya caccaki kungiyar kwadago ta ƙasa NLC kan zanga-zangar da ta yi domin nuna adawa da tsadar rayuwa da yunwa.

Shugaban ya ce ba zai yiwu NLC ta yaƙi gwamnatin da ba ta wuce wata 9 ba, yana mai cewa ba su ne kaɗai ke magana da muryar ƴan Najeriya ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel