Bayan Karkare Na Kano, Kotun Koli Ta Sanya Ranar Raba Gardama a Shari'ar Zaben Kaduna

Bayan Karkare Na Kano, Kotun Koli Ta Sanya Ranar Raba Gardama a Shari'ar Zaben Kaduna

  • Kwanaki biyu bayan yanke hukuncin zaben jihar Kano, Kotun Koli ta sanya ranar raba gardama a shari'ar zaben Kaduna
  • Kotun ta sanya ranar Alhamis 19 ga watan Janairu a matsayin ranar yanke hukuncin karshe kan takaddamar zaben
  • Wannan na zuwa ne bayan Gwamna Uba Sani ya yi nasara a Kotun Daukaka Kara a matsayin halastaccen zababben gwamna a jihar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kaduna - Kotun Koli ta sanya ranar raba gardama a shari'ar zaben gwamnan jihar Kaduna.

Kotun ta sanar da ranar Alhamis 19 ga watan Janairu a matsayin ranar yanke hukuncin da ake yi a jihar kan zaben gwamna.

Kotun Koli ta saka ranar yanke hukunci kan shari'ar zaben gwamnan jihar Kaduna
Kotun Koli za ta yanke hukunci a shari'ar Kaduna ranar Alhamis. Hoto: Uba Sani, Isa Ashiru Kudan.
Source: Twitter

Wane hukunci kotun ta yanke a baya?

Kara karanta wannan

Cikakkun sunaye: Abba Yusuf, Caleb Mutfwang da gwamnoni 8 da Kotun Koli ta tabbatyar da nasarorinsu

Isah Ashiru Kudan wanda ya yi takara a jami'yyar PDP shi ke kalubalantar zaben Gwamna Uba Sani na jam'iyyar APC a jihar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A kwanakin baya, Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da nasarar Gwamna Uba Sani a matsayin halastaccen zababben gwamna a jihar.

Har ila yau, ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Ashiru Kudan saboda rashin gamsassun hujjoji a shari'ar.

Yaushe aka yanke hukuncin zaben Kano?

Wannan na zuwa ne kwanaki biyu kacal bayan yanke hukuncin zaben gwamnan Kano da ta dauke hankulan mutane a Najeriya baki daya.

A ranar Juma'a ce 12 ga watan Janairu aka tabbatar da nasarar Gwamna Abba Kabir a matsayin halastaccen gwamnan jihar Kano.

Dan takarar jam'iyyar APC, Nasiru Gawuna shi ke kalubalantar zaben da aka gudanar a watan Maris.

A ranar Juma'a ce Kotun Koli ta yanke shari'ar zaben jihohi 8 da suka hada da Kano da Zamfara da Plateau da Bauchi.

Kara karanta wannan

Kotun Koli ta yi hukunci kan shari'ar neman tsige gwamnan APC, bayanai sun fito

Sauran sun hada da jihohin Ebonyi da Legas da Abia da Cross River wanda aka kammala a ranar.

Kotu ta yi hukunci kan shari'ar zaben jihar Kaduna

A wani labarin, Kotun Daukaka Kara da ke zamanta a Abuja ta yi hukunci kan shari'ar zaben gwamnan jihar Kaduna.

Kotun ta tabbatar da nasarar Gwamna Uba Sani na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a Kaduna.

Har ila yau, kotun ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Isa Ashiru Kudan saboda rashin hujjoji.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.