Shugaba Tinubu Ya Nada Sabbin Hadimai 18 a Ofishin Kashim Shettima

Shugaba Tinubu Ya Nada Sabbin Hadimai 18 a Ofishin Kashim Shettima

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da naɗin sabbin hadimai 18 a ofishin mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima.

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Tinubu ya amince da nadin masu ba da shawara na musamman da manyan mataimaka 18 domin aiwatar da kudirin gwamnatinsa a sassa daban-daban na tattalin arziki.

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Shugaba Tinubu Ya Nada Sabbin Hadimai 18 a Ofishin Kashim Shettima Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
Asali: Facebook

Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da Shettima ya wallafa a shafinsa na manhajar X ranar Litinin mai ɗauke da sa hannun daraktan yaɗa labarai na ofishinsa.

Sabbin hadiman sun ƙunshi masu ba da shawara na musamman 6 da manyan masu taimakawa na musamman guda 12, jumulla su 18 kenan.

Sanarwan ta ƙara da bayanin cewa dukka zasu yi aiki ne a ofishin mataimakin shugaban ƙasa domin tabbatar da kudirin "Sabunta fata" na gwamnatin Bola Tinubu.

Kara karanta wannan

Manyan Hadiman Gwamna da Wasu Jiga-Jigai Sun Ƙara Yi Wa PDP Babban Lahani, Sun Koma APC

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Jerin sunaye da muƙaman sabbin hadiman

Legit Hausa ta tattaro muku sunaye da muƙaman sabbin hadiman guda 18, ga su kamar haka:

1. Rukaiya El-Rufai - Mai bada shawara ta musamman kan NEC da sauyin yanayi

2. Tope Kolade Fasua - Mai bada shawara na musamman kan harkokin tattalin arziƙi.

3. Aliyu Modibbo Umar - Mai bada shawara na musamman kan ayyuka

4. Hakeem Baba Ahmed - Mai bada shawara na musamman kan harkokin siyasa

5. Jumoke Oduwole - Mai bada shawara na musamman kan PEBEC da hannun jari

6. Sadiq Wanka - Mai bada shawara na musamman kan samar da wutar lantarki

7. Usman Mohammed - Babban Mataimaki na musamman kan harkokin Gudanarwa

8. Kingsley Stanley Nkwocha - Babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai da sadarwa.

9. Ishaq Ahmed Ningi - Babban mataimaki na musamman kan kafofin watsa labarai da ayyukan gaggawa

Kara karanta wannan

Magana Ta Fito: Na Kusa da Atiku Abubakar Ya Tona Asirin Gwamnatin Shugaba Tinubu Kan Abu 1 Tal

10. Peju Adebajo - Babban mataimaki na musamman kan Zuba Jari da cefanar da kayayyaki

11. Mohammed Bulama - Babban mataimaki na musamman kan Ayyuka na Musamman

12. Kingsley Uzoma - Babban mataimaki na musamman kan Kasuwancin Noma da samarwa

13. Gimba Kakanda - Babban mataimaki na musamman kan nazari da Bincike

14. Temitola Adekunle-Johnson - Babban mataimaki na musamman kan Samar da Ayyuka da MSMEs

15. Nasir Yammama - Babban mataimaki na musamman kan harkokin kirkire-kirkire

16. Zainab Yunusa - Babbar mataimakiya ta musamman kan majalisar tattalin arziki NEC

17. Mariam Temitope - Babbar mataimakiya ta musamman kan shirye-shiryen raya yanki

18. Bashir Maidugu - mataimakin mai ba shugaban kasa shawara (Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa).

Sanatan Jam'iyyar PDP a Jihar Edo Ya Sake Koma Wa Jam'iyyar APC

A wani rahoton na daban Tsohon ɗan majalisar dattawan Najeriya, Sanata Mathew Urhoghide, ya sake koma wa jam'iyyar APC.

Kara karanta wannan

Sabuwar Matsala Ta Ɓullo Wa Shugaba Tinubu Kan Naɗa Gwamnan Babban Banki CBN

Sanata Urhoghide ya tattara kayansa ya fice daga jam'iyyar PDP zuwa APC ne ranar Litinin, 18 ga watan Satumba, 2023.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262