Sanatoci Sun Tantance Mutum 45, An Dakatar da El-Rufai, Mutum 2 a Ministoci

Sanatoci Sun Tantance Mutum 45, An Dakatar da El-Rufai, Mutum 2 a Ministoci

  • Sanatoci sun gama aiki a kan mutanen da aka gabatar masu domin ba su mukamin Ministoci a Najeriya
  • Nasir El-Rufai da Abubakar Sani Danladi su na cikin wadanda ba a gamsu da su a Majalisar dattawa ba
  • Sanatoci sun jingine Stella Erhuvwu Okotete wanda kafin yanzu ta rike shugabancin bankin NEXIM

FCT Abuja - Majalisar Dattawa ta kammala aikin tantance wadanda ake so su zama Ministocin tarayya, kuma ta gabatar da sunayen dukkansu.

Tashar NTA ta kawo jerin sunayen wadanda Sanatoci su ka amince da su, su ka gamsu Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada a gwamnatinsa.

Abin da ya ba mutane matukar mamaki shi ne yadda aka nemi sunayen wasu fitattun mutane a cikin wadanda aka gabatar, amma aka rasa.

Ministoci
Majalisa ta tantance Ministoci Hoto: President of the Senate
Asali: Facebook

El-Rufai da mutum 2

Majalisar dattawa ba ta amince da tsohon Gwamna Malam Nasir El-Rufai ba duk an tantance shi.

Kara karanta wannan

Mariya Bunkure ta Bayyana a Majalisa, Ta Canji Maryam Shetty a Sahun Ministoci

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Da ya bayyana a gaban majalisa, an ji yadda El-Rufai ya amsa tambayoyi, sai dai tun a lokacin aka samu labari akwai korafin da aka shigar a kan shi.

A baya, an taba samun wata kungiya da ta kai karar Okotete gaban CCB, ana zargin ‘yar siyasar da kin fadawa hukumar gaskiyar abin da ta mallaka.

Shi kuwa Sanata Abubakar Sani Danladi an san cewa ana zargin kotu ta hana masa rike duk wani mukami, sai dai ‘dan siyasar ya musanya ikirarin.

Idan aka tafi a haka ba tare da ta canza zani ko an bada sunan wani dabam ba, jihar Kaduna za ta kasance ba ta da wakicli a majalisar zartawa ta FEC.

Wadanda aka tantance

1. ABUBAKAR KYARI

2. ABUBAKAR MOMOH

3. NYESOM WIKE

Kara karanta wannan

Ministoci: Sanatoci sun Tantance Mutum 46, Jami’an Tsaro na Binciken Ragowar 2

4. PROF. JOSEPH UTSEV

5. JOHN ENO

6. BELLO MOHAMMED

7. MOHAMMED BADARU ABUBAKAR

8. YUSUF MAITAMA TUGGAR

9. UJU KEN OHANEYE

10. OLUBUNMI TUNJI OJO

11. NKEIRUKA ONYEJEOCHA

12. BETTA EDU

13. IMAAN SULEIMAN

14. DAVID UMAHI

15. ADEBAYO OLAWALE EDUN

16. AHMAD DANGIWA

17. UCHE NNAJI

18. DELE ALAKE

19. WAHEED ADEBAYO ADELABU

20. MUHAMMAD IDRIS

21. PROF. ALI PATE

22. DR. DORIS UZOKA

23. LATEEF FAGBEMI (SAN)

24. EKPERIKPE EKPO

25. HANNATU MUSAWA

26. IBRAHIM GEIDAM

27. ALIYU SABI ABDULLAHI

28. HEINEKEN LOKPOBIRI

29. ALKALI AHMED SA'EED

30. DR. YUSUF TANKO SUNUNU

31. ATIKU BAGUDU

32. BELLO MATAWALLE

33. ADEGBOYEGA OYETOLA

34. SIMON LALONG

35. ABDULLAHI TIJJANI GWARZO

36. BOSUN TIJJANI

37. DR MARIYA MAHMOUD

38. DR ISIYAKA SALAKO

39. DR TUNJI ALAUSA

40. LOLA ADE JOHN

41. PROF. TAHIR MAMMAN

42. ZEPHANIAH JISSALO

43. UBA MAIGARI AHMADU

44. SHUAIBU ABUBAKAR AUDU

45. FESTUS KEYAMO (SAN)

Tinubu bai tsira ba

Rahoto ya zo kwanaki cewa wasu mutanen yankin Arewa sun soki Mai girma shugaban kasa da cewa bai zabo masu wakilai na kwarai ba.

Dama an ce ba a iyawa ‘Dan Adam domin ana tuhumar Tinubu da dauko kwararru daga jihohin Kudu da tattara tsohon Gwamnoni daga Arewa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel