Tashin Hankali Yayin Da ’Yan Daba Suka Farmaki Kwamishina a Jihar Arewa, Sun Sace Motarsa

Tashin Hankali Yayin Da ’Yan Daba Suka Farmaki Kwamishina a Jihar Arewa, Sun Sace Motarsa

  • Yayin da ake ci gaba da zaman dar-dar a jihar Adamawa, wasu ‘yan daba sun farmaki kwamishinan Muhalli a jihar
  • Mohammed Sadiq ya gamu da tsautsayin ne a daren jiya Lahadi 11 ga watan Faburairu a gidansa da ke birnin Yola na jihar
  • Rahotannin sun tabbatar da cewa kwamishinan ya samu raunuka wanda yanzu haka ya na asibiti mai zaman kansa a Yola

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Adamawa – Wasu da ake zargin ‘yan daba ne sun kai farmaki kan kwamishinan Muhalli a jihar Adamawa.

Maharan sun farmaki Mohammed Sadiq ne a daren jiya Lahadi 11 ga watan Faburairu tare da sace motar da yake hawa.

Kara karanta wannan

Mummunar gobara ta tashi a ofishin 'yan sandan Kano

Yan daba sun kai farmaki kan kwamishina a jihar Arewa, sun yi barna
Yan daba sun farmaki kwamishinan Adamawa tare da sace motarsa. Hoto: Mohammed Sadiq.
Asali: Facebook

Yadda 'yan daban suka farmaki kwamishinan

Bayan harin, rahotannin sun tabbatar da cewa kwamishinan ya samu raunuka wanda yanzu haka ya na asibiti mai zaman kansa a Yola.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

An tabbatar da cewa maharan sun kai farmakin ne kan kwamishinan a gidansa da ke birnin Yola na jihar Adamawa.

Mataimakiyar gwamnan jihar, Farfesa George Farauta da wasu jami’an gwamnati sun kai ziyara wurin kwamishinan da ke kwance a asibiti.

Gwamna Finitiri ya gargadi jama'a jihar

Farauta yayin ziyarar jajen, ta yi addu’ar neman lafiya ga kwamishinan da kuma kare faruwar hakan a gaba.

Wannan hari kan kwamishinan na zuwa ne bayan Gwamna Ahmadu Fintiri ya fitar da wata sanarwa kan shirin fasa rumbun abinci a jihar.

Gwamnan ya ce wasu mutane a jihar su na daukar nauyin bata gari don kawo rashin zaman lafiya a jihar.

Kara karanta wannan

An ji kunya: Matasa masu karfi a jika sun kashe zuciyarsu, sun sace fanka a masallaci

Ana zargin hakan ne yayin da mutane ke cikin halin yunwa a kasar wanda hakan ka iya tunzura jama'a fasa rumbunan gwamnati.

A baya ma hakan ya taba faruwa a jihar inda mutane ke zargin an tara kayan abinci tun lokacin annobar 'Corona'.

DSS ta tsare Oscar a Abuja kan wani zargi

A baya, kun ji cewa hukumar tsaro ta DSS ta tsare Daraktan fina-finan Kannywood, Sunusi Oscar a Abuja.

Hukumar na zargin Oscar da furta wasu kalamai da suka shafi barazanar kisa ga wani jigo a gwamnatin Kano.

Asali: Legit.ng

Online view pixel