Yan Sandan Birtaniya Na Tuhumar Tsohuwar Ministan Man Fetur Alison-Madueke Da Cin Hanci
- 'Yan sandan Burtaniya sun gurfanar da tsohuwar ministar man fetur, Diezani Alison-Madueke a gaban kotu kan cin hanci
- 'Yan sandan sun bayyana haka a ranar Talata 22 ga watan Agusta yayin da su ke zarginta da karbar na goro
- Madueke ta kasance tsohuwar shugabar Kasashe Masu Arzikin Mai (OPEC) a lokacin mulkin Goodluck Jonathan
DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!
Landan - Wani sabon rahoto ya tabbatar da cewa 'yan sanda a Burtaniya sun gurfanar da tsohuwar ministar man fetur, Diezani Alison-Madueke a gaban kotu kan cin hanci.
Wannan na zuwa ne bayan yin bincike da Hukumar Laifuka ta Kasa (NCA) ta yi kamar yadda Reuters ta tattaro.
!['Yan sandan Burtaniya sun kama Diezani Alison-Madueke 'Yan sandan Burtaniya sun kama Diezani Alison-Madueke](https://cdn.legit.ng/images/1120/51733776093d99a0.jpeg?v=1)
Asali: Twitter
NCA ta ce Diezani ta karbi cin hanci a lokacin da ta ke rike da mukamin ministar man fetur don karbar kwantiragi na miliyoyin Daloli, Legit.ng ta tattaro.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/2954d91479167554.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Imaan Suleiman: Abubuwa 10 Muhimmai Game Da Mace Ta Farko A Matsayin Ministan Harkokin 'Yan Sanda
Meye ake zargin Diezani a kai?
Shugaban hukumar NCA, Andy Kelly ya ce:
DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar
"Mu na zargin Diezani Alison-Madueke da karbar na goro don ba da kwantiragin miliyoyin Daloli a lokacin da ta ke rike da mukamin ministar man fetur a Najeriya."
Ana zargin ta samu kusan Yuro dubu 100 da wasu motoci da kuma jiragen hawa don shakatawa da iyalanta da kuma amfani da wasu kadarori na birnin Landan.
A ina Diezani ta ke?
Madueke wacce ke zaune a St. John's Wood da ke Landan za ta gurfana a gaban kotun majistare a birnin a ranar Litinin 2 ga watan Oktoba na sheakrar 2023.
Madueke mai shekaru 63 ta kasance cikin masu ruwa da tsaki a gwamnatin tsohon shugaban kasa, Goodluck Ebele Jonathan.
Ta rike ministan arzikin man fetur daga shekarar 2010 zuwa 2015, ta kuma rike mukamin shugabar Kungiyar Kasashe Masu Arzikin Mai (OPEC).
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/79bb36925926769b.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Meye zai faru? Shugaban matasan PDP ya bayyana kwarin gwiwar tsige Tinubu a mulki
Kotu Ta Umarci Kwace Kadarorin Diezani A Abuja
A wani labarin, Babbar kotun Tarayya da ke birnin Abuja ta ba da umarnin kwace dukkan kadarorin tsohuwar ministar man fetur, Diezani Alison-Madueke.
Mai Shari'a Mobolaji Olajuwon ta ba da wannan umarnin ne a ranar 24 ga watan Oktoba na 2022 a Abuja.
Cikin kadarorin da za a kwace akwai fuloti mai lamba 1854 da ke kan titin Muhammad Mudashir da kuma mai lamba 6 da titin Aso da ke yankin Maitama da Asokoro.
Asali: Legit.ng