Kannywood: Yadda Jarumi Adam A Zango Ya Auri Maimuna da Mata 6 daga 2007 zuwa 2025

Kannywood: Yadda Jarumi Adam A Zango Ya Auri Maimuna da Mata 6 daga 2007 zuwa 2025

  • Amina Uba Hassan (Maman Haidar) ita ce matar Adam A Zango ta farko, kuma mabudin aure-aure bakwai da jarumin ya yi a shekaru 19
  • A kaf cikin mata shida da ya aura kafin aurensa na bakwai a 2025, Zango ya ce rabuwa da Safiyya Chalawa ne ya jefa shi a damuwa
  • A wannan rahoton, Legit Hausa ta kawo muhimman abubuwan sani game da mata bakwai da jarumi Zango ya aura daga 2006 zuwa 2025

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Kaduna - A watan Agusta 2025, fitaccen jarumin Kannywood kuma mawaki Adam A. Zango ya sake shiga sabon babi na rayuwarsa ta aure.

Legit Hausa ta ruwaito cewa Adam A Zango ya angwance da amaryarsa Maimuna Musa, wadda aka fi sani da suna Salamatu a shirin Garwashi.

Kara karanta wannan

Fusatattun matasa sun yi ajalin mata a Najeriya kan zargin batanci ga Manzo SAW

Yadda Adam A Zango ya auri mata 7 a daga 2006 zuwa 2025
Maryam AB Yola, da Adam A Zango tare da Safiyya Chalawa, da Maimuna Musa. Hoto: Adam A Zango, Maryam Yola, Maimuna Musa
Source: Facebook

Mai shirya fim din Garwashi, Fauziyya D. Sulaiman, ta yi matukar murna da wannan auren, inda har ta nemi jin ra'ayoyin mutane kan jarumar da za ta maye gurbin Salamatu a shirin.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hajiya Fauziyya ta shaida wa Legit Hausa cewa, irin wannan auratayyar tsakanin jarumai ne zai kara wa masana'antar kima a idon jama'a.

"Wannan abin so ne, kuma su duka biyun sun yi abin da ya dace. Muna yi masu addu'ar Allah ya ba su zaman lafiya, ya kawo zuriya ta gari."

- Fauziyya D. Sulaiman.

Game da shawarwarin da take ganin za ta iya ba ma'auratan, 'Uwar marayu' kamar yadda ake kiranta, ta ce:

'Ni shawara ta gare su baki daya shi ne su ji tsoron Allah, don shi aure ibada ne, idan aka rike shi a matsayin ibada, to za a ga daidai. Allah ya ba su zaman lafiya."

Wannan sabon aure na Adam A Zango ya sake jawo hankalin jama’a, musamman ganin yadda tarihin aurensa ya taba janyo cece-kuce a baya.

Kara karanta wannan

Lahadi: Ruwan sama da iska mai ƙarfi zai sauka a Abuja, Neja, Yobe da wasu jihohi

Zango: Jarumin da ya zarce sa'a a Kannywood

'Baba Ado' kamar yadda wasu a Kannywood ke kiransa, ya fara shahara tun farkon shekarun 2000, kuma tun daga lokacin ya gina kansa a matsayin ɗaya daga cikin manyan jarumai a fina-finan Hausa.

A cewar wani rahoton da aka wallafa a shafin Wikipedia, Adamu ya fito a fina-finai sama da 100, ya rera wakoki da dama, sannan ya kafa kamfaninsa na Zango Production.

Baya ga fim, Adam A Zango ya yi fice a waka da rawa, ya kuma lashe lambobin yabo da dama a harkokin nishadi a Arewa.

Wannan ya tabbatar da matsayinsa a matsayin jarumin da tasirinsa ya zarce Kannywood zuwa kasashen waje, domin ya sha fita waje yin wasanni.

Mata 7: Tarihin auren Adam a Zango

Tarihin aurensa shi ne mafi daukar hankali a rayuwarsa ta sirri. A cikin rahoton Daily Trust na 2022, an bayyana cewa ya yi aure sau da dama tun daga 2007.

Kara karanta wannan

Borno: Mayakan boko haram sun yi wa matafiya kwantan bauna, sun bude wa motarsu wuta

Legit Hausa ta tattaro bayanai game da mata 7 da Adam A Zango ya aura daga shekarar 2007 zuwa 2025:

1. Amina Uba Hassan

Amina Uba (Maman Haidar) ita ce matar Adam A Zango ta farko, wacce ya aure ta a 2007.
Jarumi Adam A Zango, da jaruma Amina Uba Hassan. Hoto: Adam A Zango, Laila Adam
Source: Facebook

Amina Uba Hassan (Maman Haidar) ita ce matar Adam A Zango ta farko. An ce sun yi aure ne tun a shekarar 2007, kuma sun samu karuwar da namiji a 2008, Haidar.

Auren nasu bai jima suka rabu, kuma Amina ta nemi shawarar Adam A Zango kafin ta shiga harkar fim, inda a yanzu ta fito a fina finai masu yawa, ciki har da shirin Labarina.

A wata hira da ta yi a shirin Gabon's Room Talk Show na YouTube, Maman Haidar ta ce ta auri Adam A Zango ne a lokacin da ya dace, amma kuma 'na auri wanda bai dace ba, a lokacin da ya dace."

2. Aisha Muhammad daga Zaria

Bayan rabuwa da Amina, Adam ya kara aure da Aisha Muhammad, yar gari Shika da ke Zaria, jihar Kaduna.

An ruwaito cewa Aisha ta haifa wa Adam A Zango 'ya'ya uku, kafin Allah ya yi rabuwarsu bayan shekaru suna tare.

Kara karanta wannan

PDP: Gwamna Bala Ya bayyana yiwuwar takarar Shugaban kasa tare da Seyi Makinde

Rahoton jaridar Daily Trust ya tabbatar da auren a matsayin wani bangare na jerin aure-auren da jarumin ya yi.

3. Maryam daga Nasarawa

Auren na uku da jarumin Kannywood din ya yi shi ne da wata Maryam, wacce aka ce 'yar asalin jihar Nasarawa ce.

An ce wannan auren na Adam A Zango bai wani jima ba, suka rabu.

4. Maryam AB Yola

Adam A Zango da Maryam AB Yola sun yi aure a 2013 amma sun rabu bayan shekaru.
Maryam AB Yola ta haihu a gidan mijinta Muhammad | Jarumi Adam A Zango. Hoto: Maryam Yola, Adam A Zango
Source: Facebook

Wata shahararriyar mace da ta shiga jerin matan jarumi Adam A Zango ita ce Maryam AB Yola, wadda aka daura aurensu a shekarar 2013.

Wannan aure ya dauki hankalin jama’a sosai saboda Maryam AB Yola ta kasance daya daga cikin 'yan matan Kannywood da ke tashe a lokacin.

Auren jaruman biyu ya mutu cikin ruwan sanyi ba tare da duniya ta ji ba. Amma duniya ta dauka a lokacin da aka ji Maryam ta yi wani auren.

A ranar 30 ga watan Satumba, 2022, jaridar Fim Magazine ta rahoto cewa Maryam AB Yola ta amarce da mijinta, Muhammad.

Kara karanta wannan

Daga Kudu zuwa Arewa: Yadda matatar Dangote take sauya tattalin arzikin Najeriya

5. Ummul Kulsum daga Kamaru

Ummul Kulsum daga Kamaru, ita ce matar Adam A Zango ta biyar, bayan rabuwarsa da Maryam AB Yola.
Adam A Zango tare da matarsa ta biyar, Ummul Kulsum, 'yar Kamaru. Hoto: Adam A Zango
Source: Facebook

A 2015, Zango ya auri Ummul Kulsum, wata kyakkyawar mace da aka ce asalinta 'yar Jamhuriyar Kamaru ce.

Jaridar Premium Times ta rahoto cewa Adam Zango ya auri Ummul Kulsum kasa da shekara uku da rabuwarsa da Maryam AB Yola.

Kafin auren Ummul Kulsum, Zango ya fuskanci zarge-zarge daga jaruma Rahama Sadau cewa yana yi mata tayin lalata, inda har ya cire ta daga wani fim dinta saboda ba ta amince ba.

Sai dai, Adam A Zango ya karyata wannan zargi, amma daga bisani ya ba jarumar da manajansa, Ali Nuhu hakuri.

Rahoto ya nuna cewa Ummul Kulsum ce ta haifa wa jarumi Zango 'yarsa ta fari, wacce aka sanya wa suna Murjanatu.

6. Safiyya Umar Chalawa daga Kebbi

Adam A Zango ya rabu da matarsa ta shida, Safiyya Chalawa duk da alkawarin da ya dauka
Adam A Zango tare da matarsa ta shida, Safiyya Umar Chalawa, 'yar mutanen Kebbi. Hoto: Adam A Zango
Source: Facebook

A karshen watan Afrilun shekarar 2019, aka ruwaito cewa Adam A Zango ya auri matarsa ta shida, Safiyya Umar Chalawa, da aka fi sani da Suffy, 'yar jihar Kebbi.

Kara karanta wannan

Abubuwa 5 da ya kamata ku sani game da Sarkin da ya 'kunyata' Najeriya a Amurka

Rahoto ya nuna cewa an daura auren Zango da Safiyya a karamar hukumar Gwandu ta jihar Kebbi, a masallacin Juma'a na fadar sarkin Gwandu.

Auren Suffy shi ne auren Zango na shida, bayan da aure biyar da ya yi a baya ya samar da yara biyar, maza hudu da mace daya.

A lokacin da ya sanar da auren, mun ruwaito cewa, jarumin ya yi alkawarin cewa ba zai sake ta ba, za ta kasance matarsa ta har abada.

Sai dai kuma, rahoton WikkiTimes ya tabbatar da cewa aurensu ya mutu a watan Afrilun 2023 bayan matsaloli na cikin gida.

Wannan rabuwar ita ce ta fi daukar hankali saboda Safiyya ta fito daga gida mai daraja, kuma rabuwar ta tayar da kura sosai a shafukan sada zumunta.

7. Maimuna Musa – sabon babi

Adam A Zango ya auri jaruma Maimuna a matsayin mata ta bakwai
Adam A Zango a wajen biki da amaryarsa, jaruma Maimuna Musa. Hoto: Fauziyya D. Sulaiman
Source: Facebook

A watan Agusta 2025, jarumi Zango ya yi aure karo na bakwai da Maimuna Musa (Salamatu a Garwashi). Wannan aure ya zo ne bayan shekaru biyu da rabuwa da Safiyya, kuma ya sake jawo cece-kuce a Kannywood.

Kara karanta wannan

Gwamna ya samu gagarumin goyon baya, ana so ya nemi takarar shugaban kasa a 2027

Marubuciya, Uwa Aishatu Gidado ta taya su murna tare da yin nasiha, inda ta gargadi Maimuna kan tsoron Allah da girmama mijinta Zango.

Mun ruwaito cewa, Uwa Aishatu ta shawarci Zango ya rike amanar aure, ya rinka nuna kulawa ga amaryarsa, kuma wannan ya zama auren mutu-ka-raba.

Kalubalen da Adam A Zango ya fuskanta

A wata hira da aka yi da shi a Fabrairu 2024, Adam ya bayyana cewa ya fuskanci matsalar damuwa bayan rabuwarsa da Safiyya.

Ya ce wannan ya shafi aikinsa da rayuwarsa ta yau da kullum, abin da ya sa masoyansa da dama suka tausaya masa, kamar yadda muka ruwaito.

Jarumin ya kuma janye kalamansa na baya cewa ba zai sake aure ba, inda ya ce yana bukatar mace domin kare martabar iyalinsa.

Wannan ya nuna cewa duk da shahararsa, shi ma mutum ne kamar kowa da ke fuskantar ƙalubale a rayuwar aure da zamantakewa.

'Dalilin yawan mutuwar aure na' - Zango

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Adam A Zango, ya bayyana cewa, ba shi ne yake da sha'awar yin aure, yana sakin matansa ba, kaddararsa ce a hakan.

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: Shugaban Boko Haram, Bakura ya karyata labarin kashe shi

Fitaccen jarumin, ya ce Allah wannan tana daya daga cikin jarabawarsa ta rayuwa, yana mai danganta hakan da mukaddari daga Allah, abin da ba zai iya canja wa a karan kansa ba.

Adamu Zango ya yi nuni da cewa duk wani abu da ya roki Allah ya ba shi, ya samu, illa dai matar da zai aura, kuma su yi zaman aure ba tare da sun rabu ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com