Sakamakon zaben June 12 na kowacce jiha da dalilin da yasa IBB yayi watsi dashi
Kamar yadda jaridar Sahara Reporters ta ruwaito mun samo muku sakamakon zaben shugaban kasa na ranar 12 ga watan Yuni da aka yi a shekarar 1993, tsakanin jam'iyyar SDP da NRC
Sakamakon zaben ranar 12 ga watan Yuni, shekarar 1993, da aka yi watsi dashi, wanda hukumar zabe ta lokacin ta bai wa wata kotu a jihar Legas. Kamar yadda sakamakon zaben ya nuna Cif MKO Abiola ya samu kuri'u 8,341,309 a karkashin jam'iyyar SDP, hakan ya bashi damar kada abokin hamayyarsa Bashir Tofa wanda ya samu kuri'u 5,952,807 a karkashin jam'iyyar NRC.
Duba sakamakon zaben na kowacce jiha dake kasar nan a lokacin:
Abia
SDP - 105,273
NRC - 151,227
Adamawa
SDP - 140,875
NRC - 167,239
Akwa Ibom
SDP - 214,787
NRC - 199,342
Anambra
SDP - 212,024
NRC - 159,258
Bauchi
SDP - 339,339
NRC - 524,836
Benue
SDP - 246,830
NRC - 186,302
Borno
SDP - 153,496
NRC - 128,684
Cross River
SDP - 189,303
NRC - 153,452
Delta
SDP - 327,277
NRC - 145,001
Edo
SDP - 205,407
NRC - 103,572
Enugu
SDP - 263,101
NRC - 284,050
Imo
SDP - 159,350
NRC - 195,836
Jigawa
SDP - 138,552
NRC - 89,836
Kaduna
SDP - 389,713
NRC - 356,860
Kano
SDP - 169,619
NRC - 154,809
Katsina
SDP - 171,162
NRC - 271,077
Kebbi
SDP - 70,219
NRC - 144,808
Kogi
SDP - 222,760
NRC - 265,732
Kwara
SDP - 272,270
NRC - 80,209
Lagos
SDP - 883,965
NRC - 149,432
Niger
SDP - 136,350
NRC - 221,437
Ogun
SDP - 425,725
NRC - 59,246
Ondo
SDP - 883,024
NRC - 162,994
Osun
SDP - 365,266
NRC - 72,068
Oyo
SDP - 536,011
NRC - 105,788
Plateau
SDP - 417,565
NRC - 259,394
Rivers
SDP - 370,578
NRC - 640,973
Sokoto
SDP - 97,887
NRC - 372,250
Taraba
SDP - 101,887
NRC - 64,001
Yobe
SDP - 111,887
NRC - 64,061
FCT Abuja
SDP - 19,968
NRC - 18,313
Jimilla
SDP - 8,341,309
NRC - 5,952,087
KU KARANTA: Murtala: Ya sanar da kotu cewa wallahi ba zai saki matarsa ba har sai ta biyashi sadakin naira miliyan 3.5 din shi
A bayanin da tsohon shugaban kasar mulkin soja na wancan lokacin yayi, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, yayi watsi da sakamakon zaben shugaban kasar da aka gudanar a ranar 12 ga watan Yuni, shekarar 1993.
Duk da dai tsohon shugaban kasar ya bayyana cewa an gabatar da zaben cikin kwanciyar hankali, amma duk da haka yayi watsi da sakamakon zaben.
"Mun yarda cewa anyi zabe an kammala lami lafiya. Amma akwai wuraren da muke zargin an gabatar da magudin zabe. An kashe kimanin naira biliyan 2.1 wurin gabatar da zaben. Mun samu shaidu da suke nuna cewa wasu malaman zabe sun gabatar da magudin zabe, inda aka yaudaresu da kudi."
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng