Ku fidda cikin matsalolin ku, Tinubu ya fadawa su Tambuwal a Sokoto

Ku fidda cikin matsalolin ku, Tinubu ya fadawa su Tambuwal a Sokoto

Fitaccen dan siyasar nan, tsohon Gwamnan Legas kuma jigo a jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Sanata Bola Ahmed Tinubu ya fadawa Gwamnan Sokoto da ma jam'iyyar sa ta Peoples Democratic Party (PDP) a jihar Sokoto su fidda shi cikin matsalolin su.

Tinubu ya yi wannan kalaman ne a cikin wata sanarwar da ya fitar matsayin martani akan wani rubutu da wasu suka yi a jaridun kudi aka kuma wallafa inda a ciki aka zarga da yin katsalandan a harkokin siyasar jihar da ma makwaftan ta na Zamfara da Kebbi.

Ku fidda cikin matsalolin ku, Tinubu ya fadawa su Tambuwal a Sokoto
Ku fidda cikin matsalolin ku, Tinubu ya fadawa su Tambuwal a Sokoto
Asali: UGC

KU KARANTA: An jefar da jaririya da wasika mai sosa zuciya a Kaduna

A cewar tsohon gwamnan na Legas, shi kwarjinin sa da gaskiyar sa hadi da sanin siyasar sa ne kawai ke taimaka masa a siyasar Najeriya amma shi baya katsalandan ko kadan a harkokin da ba a saka shi ba.

A wani labarin kuma, Hukumar nan ta Najeriya mai zaman kanta dake da alhakin gudanar da zabe a kasar ta mayar wa da kasar Amurka martani akan zarge-zargen da ta yi na cewa zaben da ya gudana ba yi sahihancin da ake tunani can-can ba.

Tun farko dai ofishin jakadancin kasar ta Amurka ya fito da matsayar su ne game da zaben na 2019 da ya gudana a Najeriya in da suka bayyana takaicin su akan yadda suka ce an samu karacin masu kada kuri'u da kuma cinikayyar kuri'a tsakanin 'yan siyasa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng