Rashin kammala zabe: Mata sama da 1000 sun yi zanga zanga a ofishin INEC dake Sokoto

Rashin kammala zabe: Mata sama da 1000 sun yi zanga zanga a ofishin INEC dake Sokoto

Sama da mata 1000 ne suka yi zanga-zanga a ranar Talata, 12 ga watan Maris a Ofishin INEC da ke Sokoto inda suka bukaci hukumar da ta bayyana Tambuwal a matsayin zababben gwamnan jihar ba tare da bata lokaci ba.

Matan sun nemi dalilai da yasa INEC ta yanke shawaran dage zabe da Tambuwal ya lashe a matsayin ba kammalalle ba.

Yayin da yake magana a madadin mata masu zanga-zangan, Farfesa Aisha Madawaki, da Dakta Kuku Haruna, Kulu Sifawa tare da shushugaban matan, Rabi Gayawa sun bayyana cewa sun kasance a ofishin INEC don kaddamar da bakin cikinsu bisa zaben gwamnoni da aka gudanar a ranar Asabar wanda suka yi ikirarin sun lashe sannan aka bayyana a matsayin ba kammalalle ba.

Rashin kammala zabe: Mata sama da 1000 sun yi zanga zanga a ofishin INEC dake Sokoto
Rashin kammala zabe: Mata sama da 1000 sun yi zanga zanga a ofishin INEC dake Sokoto
Source: UGC

A cewar mata masu zanga-zangan, Gwamnatin Tarayya wacce jam’iyyar APC ke jagoranta tare da hukumar INEC suna juya zabbukan da PDP ta lashe tun daga 2015 a matsayin zabbuka da ba kammalallu ba.

Yayinda take ba da dalilin da yasa suka fito zanga-zangan kwansu da kwarkwatan su, wata mamba na hukumar makarantun Firamare wato State Universal Basic Education Board (SUBEB) Hajiya Fatima Illo tace babu gwamna a Najeriya dake da zuciyar shugabanci irin na Tambuwal.

KU KARANTA KUMA: Zabe: Yadda ‘yan ta-more suka kasha ‘yan sanda biyu a Sokoto – Kwamishina

Yayin da take bada goyon bayan ikirarin ta, Illo ta ce a tarihin Najeriya, gwamna Aminu Taambuwal ne kadai ne ya san martabar mata tunda har ya zabi mata uku a matsayin kwamishinoni, 4 a matsayin masu bada shawara na musamman, 6 a matsayin manyan darektoci,3 a matsayin mambobi sannan 69 a matsayin kansiloli duk a jihar.

Matan sun ce a shirye suke don cigaba da gudanar da zanga-zangan a kulla yaumin har sai hukumar INEC ta bayyana Aminu Waziri Tambuwal a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnoni da aka gudanar a ranar Asabar a jihar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng