Mayun Najeriya sun fada ma Atiku yadda zai iya kayar da Buhari a 2019

Mayun Najeriya sun fada ma Atiku yadda zai iya kayar da Buhari a 2019

- Kungiyar fararen mayu a Najeriya sun ce Atiku zai iya lashe zabe bisa sharadi guda

- Mayun sun gargadi Atiku da ya bi shawarar manya don kada ya yi irin kuskuren da Jonathan yayi a 2015

- Sun kuma gargadi INEC da kada ta bari ayi amfani da ita wajen yin magudi a zabe

Kungiyar fararen mayu a Najeriya ta gargadi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a zaben ranar 16 ga watan Fabrairu da za a yi, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da kada ya maimaita kuskuren da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan yayi a 2015, idan har yana son ya lashe zabe.

A cewar mayun, Jonathan ya ki sauraron shawarar masu hikima wanda hakan ne ya sa shi shan kaye a zaben 2015 inda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya lashe zaben.

Mayun Najeriya sun fada ma Atiku yadda zai iya kayar da Buhari a 2019
Mayun Najeriya sun fada ma Atiku yadda zai iya kayar da Buhari a 2019
Asali: Facebook

Kungiyar ta gargadi Atiku da ya dauki sharudan da aka gindaya masa idan har yana son yayi nasara a zabe mai zuwa sannan ya fitar da yan Najeriya daga yunwa da talauci wanda mumunan manufar tattalin arziki na wannan gwamnati ya jefa su a ciki.

Daily Independent ta ruwaito cewa kakakin kungiyar, Okhue Iboi, wanda yayi magana a wani hira na wayar tarho a ranar Alhamis, 3 ga watan Janairu yace ya zama dole Atiku ya dunga ziyarar coci, masallaci da kungiyar mayu domin addu’o’i na musamman idan har yana son yin nasara.

KU KARANTA KUMA: Bakare ya yi magana game da zama shugaban kasar Najeriya na 16 (bidiyo)

Ya kuma bayyana cewa jam’iyyar PDP za ta fadi zaben gwamna a jihar Ogun idan hart bata ba Sanata Buruji Kashamu tikitin takara ba.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng