Buhari zai kashe N7.3bn kan jiragen zirga-zirgar sa cikin 2019

Buhari zai kashe N7.3bn kan jiragen zirga-zirgar sa cikin 2019

- Gwamnatin tarayya ta shirya kashe naira bilyan 7.30 wajen hada-hadar shan mai da kula da jiragen zirga-zirgar Shugaba Buhari a shekarar 2019

- Bayanan yadda za a kashe wadannan makudan kudaden na kunshe a daftarin kasafin kudin wannan shekarar da aka hgabatar a kwanakin baya

- Cikin kasafin da aka ware wa jiragen, har da batun sake kayan dafe-dafen abinci, sake inganta karfin intanet da sauran su

Gwamnatin tarayya ta shirya kashe naira bilyan 7.30 wajen hada-hadar shan mai da kula da jiragen zirga-zirgar Shugaba Muhammadu Buhari a cikin shekarar 2019, jaridar Premium Times ta rwaito.

Bayanan yadda za a kashe wadannan makudan kudaden na kunshe a daftarin kasafin kudin 2019 da aka ware domin kashe wa Buhari a zirga-zirgan da jiragensa za su yi a ciki da wajen Najeriya.

Buhari zai kashe N7.3bn kan jiragen zirga-zirgar sa cikin 2019
Buhari zai kashe N7.3bn kan jiragen zirga-zirgar sa cikin 2019
Asali: UGC

Wannan adadi na nuna cewa abin da jirgin Buhari zai kashe a 2019, ya haura adadin da aka kashe a shekarar 2017 da kuma 2018.

Cikin kasafin da aka ware wa jiragen, har da batun sake kayan dafe-dafen abinci, sake inganta karfin intanet da sauran su.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: INEC ta kaddamar da kwamitoci don zaben 2019

Jiragen Shugaban Kasa su ne jirage na biyu mafi yawa a Najeriya.

Sannan kuma ana ta korafin yadda ake kashe makudan kudade a kan jirgin, fiye ma da lokacin mulkin Goodluck Jonathan.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng