2019: Masoya sun kawo karshen addu’o’in kwanaki 40 da suka yi wa Buhari (hotuna)
Shugabannin addinai a fadin kasar sun bukaci yan Najeriya da su yi wa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari gangami a zaben shugaban kasa na 2019.
Malaman addinin sun ce Shugaba Buhari ya yi namijin kokari don haka ya kamata a bari ya kammala kyawawan aikin da ya faro.
Sun isar da wannan sakon ne a ranar Laraba, 21 ga wata Nuwamba ranar kashe na addu’o’in kwanaki 40 da suka gudanar domin tazarcen shugaba Muhammadu Buhari da kuma zaman lafiya da hadin kan Najeriya a Unity Fountain.

Asali: Facebook
Kungiyar addinai daban-dab na kasa wato National Inter-Faith and Religious Organisations for Peace (NIFROP) ne suka shirya hakan a Abuja.

Asali: Facebook
KU KARANTA KUMA: 2019: APC na hararar jihohi 30 na kasar - Shettima
Da yake Magana a taron, Bishop Sunday Garuba, yace Allah zai yi maganin duk mutumin da bai saon zaman lafiya da ci gaban Najeriya.

Asali: Facebook
A nashi bangaren, Abdulgafar Sadiq (babban limamin masallacin Usman Bello) ya bukaci Musulmi da Kirista da su tanadi katin zabensu a 2019.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng