Alkawaran Gwamnatin Tarayya duk kanzon kurege ne - ASUU

Alkawaran Gwamnatin Tarayya duk kanzon kurege ne - ASUU

- ASUU sun bayyana alkawaran Gwamnatin Tarayya a matsayin kanzon kurege, cewa mambobinta ba za su bi ta kansu ba

- Kungiyar ta ce hukuncinta na umurtan mambobinta a fadin kasar na su ajiye kayan aiki a ranar Lahadi ya kasance saboda rashin kula da daukar nauyin makarantun jami’ar kasar

- Shugaban kungiyar ya kuma koka akan rage kasafin hukumar ilimi da aka yi a yan shekarun nan, inda yace hukumar ilimi na kowacce kasa ta aka fi ba muhimmanci

Kungiyar malaman jami’a (ASUU) sun bayyana alkawaran Gwamnatin Tarayya a matsayin kanzon kurege, cewa mambobinta ba za su bi ta kansu ba.

Shugaban ASUU, Farfesa Abiodun Ogunyemi, ya fadi hakan a ranar Litinin, 5 ga watan Nuwamba a lokacin wani hira da Channels Television’s a shirin Sunrise Daily.

“Mun yanke shawarar cewa alkawaran gwamnati kanzon kurege ne. Bamu damu da kowani alkawari gwamnati za ta yi ba a yanzu,” inji shi.

Alkawaran Gwamnatin Tarayya duk kanzon kurege ne - ASUU
Alkawaran Gwamnatin Tarayya duk kanzon kurege ne - ASUU
Asali: Twitter

Furucin Ogunyemi na zuwa ne kasa da sa’o’i 24 bayan kungiyar ta dauki hukunci sakamakon hanzukansu da Gwamnatin Tarayya.

KU KARANTA KUMA: APC ta yi kira ga a binciki ziyarar da Atiku ya kai Dubai

A cewar ASUU, hukuncinta na umurtan mambobinta a fadin kasar na su ajiye kayan aiki a ranar Lahadi ya kasance saboda rashin kula da daukar nauyin makarantun jami’ar kasar.

Ya kuma koka akan rage kasafin hukumar ilimi da aka yi a yan shekarun nan, inda yace hukumar ilimi na kowacce kasa ta aka fi ba muhimmanci.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa

Ko a http://twitter.com/legitnghausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Shafin NAIJ.com Hausa ya koma Legit.ng Hausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng