Da dumin sa: Aikin jigilar matafiya na jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja ya tsaya
Shugaban hukumar gwamnatin tarayya dake kula da harkokin jigilar matafi na jirgin kasa watau Nigeria Railway Corporation, NRC, mai suna Fidet Okhiria, ya sanar da tsayar da ayyukan jigilar matafiyan daga garin Kaduna zuwa Abuja har illa-ma-sha'Allahu.
Mista Fidet Okhiria ya bayyana cewa wannan matakin da hukumar ta dauka ta dauke shi ne duba da halin rashin tsaron da jihar ke fama da shi a halin yanzu kuma za su cigaba da zaran komai ya daidaita.

Asali: Twitter
Legit.ng Hausa ta samu cewa sakamakon rikicin da ake yi a jihar ta Kaduna, gwamnatin jihar a kwanan baya ta saka dokar ta baci a jihar na tsawon kwanaki kafin ta dan sassauta ta bayan samun zaman lafiya a wasu sassan jihar.
A wani labarin kuma, Da alamu dai rikicin cikin jam'iyyar dake mulki a Najeriya, ta All Progressives Congress (APC) zai dauki wani sabon salo biyo bayan labaran da muke samu na kammala shirye-shiren ficewa daga jam'iyyar da gwamnan jihar Ogun, Ibikunle Amosun yayi.
Binciken da majiyar mu ta jaridar Punch tayi dai ya bayyana cewa gwamnan yana sunsunar jam'iyyar adawa ta Democratic Peoples Party (DPP) ne kuma tuni har ma wasu makusantan sa da abokan siyasar sa sun soma shiga jam'iyyar.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng