Faransa za ta fara koyar da darasin 'Larabci' a makarantun gwamnatin kasar

Faransa za ta fara koyar da darasin 'Larabci' a makarantun gwamnatin kasar

- Gwamnatin shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, na kokari don karfafa guiwar makarantu na koyar da darasin 'Arabi' ga dalibai tun daga shekaru 6

- Gwamnatin kasar Faransa ta ce dubunnan yara na zuwa makaranta ne karkashin daukar nauyin kasashen da ke magana da yaren Larabci, a cewar jaridar WSJ

- Wasu daga cikin makarantu masu zaman kansu sun samar da masallatai don baiwa dalibai Musulmai damar koyon yaren Larabci da kuma haddace Al-Qur'ani mai girma

Kasar Faransa za ta fara koyar da darasin 'Arabi' a makarantun gwamnati na kasar don horas da dalibai dangane da harkokin addini, wanda shine hanya mafita ga makarantun da ke dauke da Musulmai a cikin kasar.

Gwamnatin shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, na kokari don karfafa guiwar makarantu na koyar da darasin 'Arabi' ga dalibai tun daga shekaru 6, kamar dai yadda jaridar The Wall Street Journal ta kasar ta wallafa rahoton hakan a ranar Laraba.

KARANTA WANNAN: NDLEA: Kafin haramta 'Codeine', Kano, Jigawa sun sha kwalba Miliyan 3

Wannan shawarar ta zo ne sakamakon yadda wasu jami'an gwamnatin Faransa suka gano cewa akwai karancin koyar da darasin a makarantun gwamnatin kasar wanda kuma hakan ya haifar sabani tsakanin Kirista da Musulmai wadanda sune masu karancin yawa a kasar.

Faransa za ta fara koyar da darasin 'Larabci' a makarantun gwamnatin kasar
Faransa za ta fara koyar da darasin 'Larabci' a makarantun gwamnatin kasar
Asali: UGC

Gwamnatin kasar Faransa ta ce dubunnan yara na zuwa makaranta ne karkashin daukar nauyin kasashen da ke magana da yaren Larabci, a cewar jaridar WSJ.

Wasu daga cikin makarantu masu zaman kansu sun samar da masallatai don baiwa dalibai Musulmai damar koyon yaren Larabci idan har malamin nada cikakken sani akan yaren yayin da kuma ake horas da wasu yadda zasu haddace Al-Qur'ani mai girma.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta NAIJ.com Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng