Sheikh Isa Ali Pantami yayi magana game da rikicin garin Kaduna
Fitaccen malamin nan na Islama kuma babban masani a harkar na'ura mai kwakwalwa, Dakta Isa Ali Pantami yayi tsokaci game da tashin hankalin da aka samu gami da asarar rayuka a garin Kaduna, jihar Kaduna a 'yan kwanakin nan da suka gabata.
Dakta Fantami wanda yayi tsokacin game da lamarin a shafin sa na dandalin sada zumuntar zamani ta Tuwita ya yi tofin Allah-tsige ga wadanda suka tada rikicin tare kuma da yin addu'ar kariyar Ubangiji daga dukkan fitintinu ire-iren su da ka iya tasowa.

Asali: Twitter
KU KARANTA: Duk wanda Najeriya ta isa ya iya canza kasa - Buhari
Legit.ng Hausa ta samu cewa da a samu barkewar rikicin kabilanci a garin na kaduna wanda yayi sanadiyyar wata hatsaniya da ta lakume rayuka da dama a garin.
Wannan dai kamar yadda muka samu har sai da ya jaza hukumomin tsaro a jihar suka sanya dokar ta-baci ta hana fita a cikin kokuwar garin kafin a samu a shawo kan matsalar.
A wani labarin kuma, Shugaban kasar Najeriya, Muhammadu Buhari a ranar Litinin ya shawarci dukkan wanda yake ganin yana da wata kasar da zai tafi ko kuma kasar ta ishe shi to hanya a bude take don ya fice ya canza kasa.
Shugaban kasar haka zalika ya kara da cewa su da ba suda wata kasa tare da sauran miliyoyin 'yan Najeriya za su zauna nan domin ganin sun gyara kasar tare da maida ta bisa tafarki madaidaici.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://web.facebook.com/legitnghausa?_rdc=1&_rdr
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng