Shugaba Buhari ya raba ma talakawa N1.5bn a jihar Bauchi

Shugaba Buhari ya raba ma talakawa N1.5bn a jihar Bauchi

A ranar Litinin, 15 ga watan Oktoba ne jami’in shirin tallafa wa talakawa ( CCT) Jibrin Yusuf ya bayyana cewa gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ta raba wa talakawa a jihar Bauchi kudi har naira biliyan 1.5.

Yusuf ya bayyana hakan ne a yayinda wakilan kungiyar manema labarai mata na kasa (NAWOJ) suka kai masa ziyara a ofishin sa da ke garin Bauchi.

Ya ce shirin CCT ta fara raba wadannan kudade ne tun a farkon shekarar nan zuwa wannan lokaci. Sannan yace shirin za ta saka wasu talakawa 2,969 domin su samun wannan tallafi.

Shugaba Buhari ya raba ma talakawa N1.5bn a jihar Bauchi
Shugaba Buhari ya raba ma talakawa N1.5bn a jihar Bauchi
Asali: UGC

A kashe shugaban kungiyar NAWOJ Bulak Afsa ta bayyana cewa sun zo ne domin jinjina wa shirin CCT bisa wannan kokari da suke yi wa talakawa a wannan jiha.

KU KARANTA KUMA: APC ce babban adawar kanta da kanta - Atiku

A baya Legit.ng ta rahoto cewa daraktan kungiyar kamfen din Buhari, Mista Festus Keyamo (SAN) ya bayyana cewa tattalin arzikin Najeriya ne mafi inganci a nahiyar Afrika.

Keyamo ya bayyana hakan yayinda yake Magana a shirin gidan Channels TV a ranar Litinin, 15 ga watan Oktoba.

Ya ce a cikin kasashe 11 da suka shiga koma bayan tattalin arziki a fadin duniya, Najeriya duk ta fi su bunkasa ta fannin ci gaban kididdiga.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng