Zabukan 2019: Jerin gwamnonin Arewa 5 da ka iya faduwa zaben 2019

Zabukan 2019: Jerin gwamnonin Arewa 5 da ka iya faduwa zaben 2019

- Yayin da zabukan shekarar 2019 ke ta kara karatowa, yanyin siyarar na ta kara daukar zafi a dukkan fadin kasar musamman ma a yankin mu na Arewacin Najeriya.

- A bisa al'ada dai, dukkan gwamnan da ke kan yin wa'adin mulkin sa na farko yakan sake neman tsayawa takarar domin yin wa'adin mulki na biyu a kasar.

Ga dai jerin wasu gwamnonin kasar nan a yankin Arewa da masu fashin baki da tsokaci a kan al'amurran yau da kullum suke ganin da wuya su sake lashe zaben su a 2019 din saboda dalilai da dama.

Zabukan 2019: Jerin gwamnonin Arewa 5 da ka iya faduwa zaben 2019
Zabukan 2019: Jerin gwamnonin Arewa 5 da ka iya faduwa zaben 2019

KU KARANTA: An hana kafa allon kamfe din Dankwambo a jihar Adamawa

1. Abdullahi Umar Ganduje daga jihar Kano: Shi dai Ganduje ana tunanin sabanin sa da tsohon gwamnan jihar Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso zai iya kawo masa cikas a siyasar jihar.

2. Abubakar Badaru daga jihar Jigawa: Ana ganin saboda yadda 'yan adawa da tsohon gwamnan jihar Sule Lamido ke jagoranta ke da matukar karfi, za su iya kayar da shi.

3. Yahaya Bello daga jihar Kogi: Shi ma dai karfin 'yan adawar dake a jihar ne ake tunanin zai iya bashi matsala.

4. Samuel Ortom daga jihar Benue: Shi kuma wannan gwamnan kashe-kashen da ake ta fama da shi a jihar ne ake tunanin zai bashi matsala.

5. Nasiru El-rufai. Daga jihar Kaduna: Shi ma dai ana ganin duk da zaman sa dan lele a wurin shugaban kasa, 'yan adawa a jihar za su iya bashi mamaki.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng