Dangote ya kaddamar da rukunin gidaje 200 da ya ginawa ‘yan gudun hijira a Maiduguri, duba hotunan

Dangote ya kaddamar da rukunin gidaje 200 da ya ginawa ‘yan gudun hijira a Maiduguri, duba hotunan

A jiya, Litinin, ne shugaban rukunin masana’antun Dangote, Aliko Dangote, ya kaddamar da rukunin gidaje 200 na farko da gidauniyar Dangote ta ginawa mazauna sansanin ‘yan gudun hijira dake Maiduri, jihar Borno.

Dangote ya kaddamar da rukunin gidaje 200 da ya ginawa ‘yan gudun hijira a Maiduguri, duba hotunan
Rukunin gidaje 200 da Dangote ya ginawa ‘yan gudun hijira a Maiduguri

Dangote ya kaddamar da rukunin gidaje 200 da ya ginawa ‘yan gudun hijira a Maiduguri, duba hotunan
Dangote yayin kaddamar da rukunin gidaje 200 da ya ginawa ‘yan gudun hijira a Maiduguri

Dangote ya kaddamar da rukunin gidaje 200 da ya ginawa ‘yan gudun hijira a Maiduguri, duba hotunan
Dangote yayin bayar da takardar mallaka ga wata mata

Dangote ya kaddamar da rukunin gidaje 200 da ya ginawa ‘yan gudun hijira a Maiduguri, duba hotunan
Dangote ya kaddamar da rukunin gidaje 200 da ya ginawa ‘yan gudun hijira a Maiduguri

Tun a jiya ne Legit.ng ta kawo maku labarin cewar, hamshakin attajiri Aliko Dangote ya kaddamar da wasu sabbin gidaje guda 200 da ya gina ma yan gudun hijira, musamman matan da suka rasa mazajensu a hannun Boko Haram, da kuma kananan yara da rikicin ya mayar dasu marayu.

DUBA WANNAN: Abinda kasar Amurka ta fada a kan harin da 'yan Boko Haram suka kai garin Damboa a jihar Borno

Kamfanin dillancin labaru, NAN, ta ruwaito kimanin shekaru biyu da suka gabata ne Dangote yayi wannan alkawari, inda ya cika shi a yanzu, kamar yadda ya bayyana a ranar Litinin, 18 ga watan Yuni a jihar Borno a yayin kaddamar da gidajen.

A shekaru biyu da suka wuce na dauki wannan alkawari a yayin wata ziyara da na kai sansanin yan gudun hijira, manufar wannan abin alheri shi ne don tallafa ma kokarin da gwamnati ke yi na sake gina ma yan gudun hijira gidajensu da yan Boko Haram suka lalata"' a cewar Dangote

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel