Jam'iyyar PDP
Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kogi a karkashin PDP, Sanata Dio Melaye, ya yi kalamai masu kaushi kan tsohuwar jam'iyyarsa. Ya ce ta koma hannun APC.
Gwamna Ademola Adeleke na jihar Osun ya karyata rahotannin da ke yawo cewa ya gama shirin shiga jam'iyyar haɗaka ADC, ya ce yana nan daram a PDP.
A labarin nan, za a ji jam'iyya mai mulki a Kano, NNPP ta caccaki PDP tare da zargin cewa ita ce ta lalata abubuwa da dama a jihar tun a shekarun baya.
A labarin nan, za a ji cewa jam'iyyar PDP reshen jihar Kano ta barranta kanta da duk wata haɗakar adawa, musamman ta ADC da Atiku Abubakar ya tafi.
Dino Melaye da wasu manyan aminan siyasar tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar sun fice daga PDP sannan sun koma jam'iyyar hadaka ta ADC. Legit ta jero su.
Sanata Dino Melaye ya fice daga jam'iyyar PDP saboda rashin tasirin magance matsalolin Najeriya. Ya zargin wasu 'yan jam’iyyar da jefa ta cikin halin da ta ke ciki.
Tsohon ministan yaɗa labarai, Farfesa Jerry Gana ya bayyana cewa Peter Obi zai iya tumurmusa duk wani ɗan siyasa a Arewacin Najeriya idan ya tsaya takara a PDP.
Tsohon dan takarar shugaban kasa na LP, Peter Obi ya musanta jita-jitar da ke yawo cewa ya gama shirin sauya sheka zuwa ADC, ya ce yana nan a haɗakar ADC.
Yayin da ake shirin kawo sauyi kan zaben 2027, APC da wasu 'yan majalisa sun nuna rashin goyon baya, suna cewa hakan zai haifar da cikas ga INEC da tsarin zabe.
Jam'iyyar PDP
Samu kari