Masu Garkuwa Da Mutane
Wasu 'yan bindiga da ake zaton masu garkuwa ne sun sace matar wani basarake a jihar Kaduna. An kashe daya daga cikin wandanda suke je ceto matar sarkin a daji.
Rundunar sojin Najeriya ta kama wani dan bindiga da aka dade ana nema ido rufe mai suna Dogo a jihar Taraba. An kama wani mutum mai karya soja a Taraba.
Yayin da sace-sacen al'umma ya yi ƙamari a Edo, Gwamnan Monday Okpebholo, ya dakatar da sarkin Uwano, Dr. George Egabor, bisa yawaitar garkuwa da mutane.
Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo, ya bayyana cewa za a yanke hukuncin kisa ga duk wani mai garkuwa da mutane da aka samu da aikata laifin a jihar.
Fusatattun matasa sun kai farmaki garuruwan Fulani a Kaiama, jihar Kwara, bisa zargin suna taimaka wa 'yan bindiga; an kama masu garkuwa da mutane tara a Ekiti.
Rahotanni sun bayyana yadda babban jigo a jam'iyyar APC, Rauf Adeniji ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane, bayan sace shi a watan Janairun shekarar 2025.
Rundunar 'yan sanda ta ceto mutane 17 da aka sace a jihar Kaduna tare da kwato manyan bindigogi har 21 a cikin wata motar haya. Sun gwabza fada da yan fashi.
Jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya ta dauki matakin rufe hedkwatarta ta kasa har na tsawon wani lokaci. APC ta dauki matakin ne kan kisan da aka yi wa daraktan ta.
Jami'an tsaro sun yi nasara a kan wasu miyagun 'yan ta'adda da suka kutsa kauyen Mahume dake Dandume a jihar Katsina, tare da sace mutane shida daga gidajensu.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari