Masu Garkuwa Da Mutane
Jami'an tsaro sun samu nasarar hallaka wani tantirin dan ta'adda a jihar Kwara. Dan ta'addan ya kware wajen yin garkuwa da mutane don neman kudin fansa.
Rundunar ’yan sanda a Bauchi ta ceci mutane biyu da aka sace a Alkaleri, ta kuma cafke mutum uku da ake zargi da garkuwa yayin da ake ci gaba da neman sauran miyagu.
'Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun kai hari Filato sun sace dan majalisa mai wakiltar Pankshin, Hon Laven Denty. Har yanzu ba a samu bayanin 'yan sanda ba.
Wasu miyagun yan bindiga da ba a san manufarsu ba sun yi awon gaba da matar fasto a yankin karamar hukumar Obi da ke jihar Nasarawa, sun hada da wata bakuwa.
'Yan bindiga sun sace wata daliba da kuma wata 'yar bautar kasa a Jos, inda suka buƙaci N50m a matsayin kuɗin fansa, lamarin da ya haifar da tashin hankali a yankin.
Gwamnatin Imo ta yi alƙawarin ceto tsohon ɗan majalisar jihar, Ngozi Ogbu, wanda wasu mayaka masu fafutukar kafa Biyafara suka sace shi, tare barazanar kashe shi.
Kungiyar KADA da ke karamar hukumar Kanam a jihar Filato ta tabbatar da cewa yan bindiga sun kashe Sarkin Shuwaka, Malam Hudu Barau bayan sace shi.
'Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun kewaye wani masallaci a jihar Zamfara sun sace masallata 40 ana tsaka da sallar Asuba. Sun tafi da masallata dajin Tsafe.
Yan bindiga sun shiga kauyuka biyu a kananan hukumomin Makarfi da Kudan da ke jihar Kaduna, sun yi garkuwa da wani dan siyasa da ya yi fice a yankin.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari