Ma'aikatar Ilimin Najeriya
Allah ya yi wa wata malamar makaranta Misis Oluwatosin Aina rasuwa a jihar Ogun bayan da ta fadi ta ce ga garinku a kusa da motarta tana kokarin zuwa asibiti.
Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya sanya dokar ta baci a bangaren ilimi a kokarin ceto jihar daga durkushewa, ya kuma kwace lasisin makarantu masu zaman kansu.
Ayyukan sun tsaya cik a BUK, makarantun firamare da sakandire da ma'aikatun gwamnati a jihar Kano yayin da NLC ta tsunduma yajin aiki ranar Talata, 14 ga Nuwamba.
A baya-bayan nan Gwamnatin Tarayya da na wasu jihohi sun mayar da kwalejojin fasaha da ilimi zuwa jami'o'i sai dai hakan bai yi wa tsohon shugaban ASUP dadi ba.
Jami'an 'yan sanda sun yi nasarar kamo daliban firamare 2 da suka cinna wa makarantarsu wuta a jihar Ogun, rundunar ta ce ta fara bincike kan wannan danyen aiki.
Wasu malamai sun yi ta dukan dalibi har sai da ya rasa ransa a wata makaranta a Zaria da ke jihar Kaduna, wasu masana sun ba da shawara kan ladabtar da dalibai.
Shugaban kasa, Bola Tinubu ya kawo tsarin bai wa dalibai lamunin karatu don inganta harkar ilimi a kasar, dalibai na dakon fara wannan shirin na ba da lamuni.
Shugaban Jami'ar Abuja, Farfesa Abdul-Rasheed Na'Allah ya bayyana cewa daga yanzu sai an yi wa dukkan dalibai gwajin kwayoyi kafin ba su gurbin karatu a Jami'ar.
Kungiyar Malaman Jami'o'i ta ASUU ta bayyana cewa dalibai da dama ka iya barin karatu idan har gwamnati ba ta dauki matakin kare-karen kudin makaranta da ta ke ba.
Ma'aikatar Ilimin Najeriya
Samu kari