Yan bindiga
Wasu 'yan bindiga sun kai mummunan hari sakatariyar jihar Kuros Riba inda su ka bindige wani akanta a ma'aikatar ilimi a jihar, maharan sun biyo shi tun daga banki.
Wasu tsagerun yan bindiga sun tarfa wasu manoma biyu a gonakinsu a yankin Yangtu da safiyar ranar Talata a jihar Taraba sun yi ajalinsu, mutane sun ruɗe.
Wasu miyagun yan bindiga sun yi musayar wuta da jami'an tsaro a birnin Asaba, babban birnin jihar Delta, inda suka halaka mataimakin sufeton yan sanda (DSP).
Yan Boko Haram sun farmaki wasu masu sana'ar itace a Damboa, jihar Borno a ranar Litinin inda suka yi gunduwa-gunduwa da sassan jikin mutum sha daya.
Tsagerun yan bindiga sun yi garkuwa da akalla mutum 100 bayan sun farmaki wasu kauyuka a jihar Katsina da karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara saboda haraji.
Tsagerun yan bindiga sun yi ajalin jami'an hukumar yan sanda biyu da farar hula mutum ɗaya yayin da suka kai hari kan shingen binciken ababen hawa a jihar Imo.
Wasu 'yan bindiga sun harbe wani mai sarautar gargajiya a jihar Imo mai suna Eze Joe Ochulor da ke sarautar Otulu a karamar hukumar Ezinihite Mbaise a jihar Imo.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar fatattakar miyagun yan bindiga a wani sumame da suka kai a maboyarsu da ke jihar Kebbi. Sun ceto mutum shida.
Tsagerun yan bindiga sun kai farmaki tare da kashe mutane 20 a yankunan Yangtu da Ussa da ke jihar Taraba, a yammacin ranar Juma'a, 24 ga watan Nuwamba.
Yan bindiga
Samu kari