Matsin tattalin arziki
Shugaba Bola Tinubu ya sha alwashin cigaba da ayyukan alheri ko da kuwa za a ci gaba da korafi inda ya shawarci jami'an tsaro kan gudanar da ayyukanau.
Yayin da ake bikin ranar dimukraɗiyya, Bola Tinubu ya sanar da shirin bashi na musamman ga matasa, wanda zai fara a watan Yuli, domin tallafa wa matasa 400,000.
Rahoton SBM Intelligence ya nuna sauyin yanayi da rashin tsaro sun lalata noma a Najeriya, inda ambaliya da zaizayar ƙasa suka shafi miliyoyin mutane da gonaki.
Bayan shafe shekaru 20 yana jagorancin kamfanin sukari, Attajiri a Nahiyar Afirka gaba daya, Alhaji Aliko Dangote ya ajiye muƙaminsa a matsayin shugaba.
Kungiyar 'APC Patriotic Volunteers' ta taso gwamna Abba Kabir Yusuf a gaba inda take zargin gwamnatin Kano da karɓar bashin $6.6m ba tare da wani aiki ba.
Matasan Najeriya sun ce za su yi zanga zanga a jihohi 20 da suka hada da Kano, Bauchi Yola, Legas da birnin tarayya Abuja. Za a yi zanga zanga a ranar 12 ga Yuni
Ministan matasa a Najeriya, Ayodele Olawande ya rattaba hannu kan yarjejeniya da 'Investonaire Academy' domin horas da matasa 100,000 duk shekara kan kasuwanci.
A labarin nan, za ku ji manyan bangarorin da gan adawa da kungiyoyi ke ganin gazawar gwamnatin APC, a karkashin Bola Ahmed Tinubu a cikin shekaru biyu na mulkinsa.
Jam'iyyar PDP ta bukaci shugaban kasa Bola Tinubu ya rage kudin man fetur da kudin lantarki. PDP ta ya 'yan Najeriya murnar zuwan babbar sallah a Najeriya.
Matsin tattalin arziki
Samu kari