Shugaban Kasa a 2023: Atiku Zai Lashe Zabe a Arewa Ta Tsakiya, Inji Tsohon Minista

Shugaban Kasa a 2023: Atiku Zai Lashe Zabe a Arewa Ta Tsakiya, Inji Tsohon Minista

  • Wani tsohon minista ya nuna kwarin gwiwa cewa dan takarar PDP, Atiku Abubakar, zai lashe babban kaso a arewa maso gabas
  • Yan kwanaki kafin zaben shugaban kasa, Musa Elayo, ya tabbatar da cewar Atiku zai yi gagarumin nasara a yankin saboda goyon bayan da yake da shi
  • Elayo ya bayyana cewa arewa ta tsakiya ta PDP ce kuma jam'iyyar ta shirya kwato ta a ranar Asabar, 25 ga watan Fabrairu

Tsohon karamin ministan shari'a kuma mamba a kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na PDP, Musa Elayo, ya nuna yakinin cewa dan takararsu zai lashe zabe a arewa ta tsakiya, rahoton Leadership.

Gabannin babban zaben na ranar 25 ga watan Fabrairu, masu nazari kan harkokin zabe sun bayyana arewa ta tsakiya a matsayin filin daga ga manyan yan takarar babban kujera ta daya a kasar.

Kara karanta wannan

2023: Jerin Sunayen Manyan Malaman Addini Da Ke Takara a Zabe Mai Zuwa

Atiku ABubakar
Shugaban Kasa a 2023: Atiku Zai Lashe Zabe a Arewa Ta Tsakiya, Inji Tsohon Minista Hoto: Atiku Abubakar
Asali: Facebook

Tsohon minista ya bayyana yankin da Atiku zai lashe

A yanzu haka, jam'iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki ce ke iko a jihohin yankin baya ga Benue, inda Samuel Ortom na PDP ke a matsayin gwamna.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Sai dai kuma, Elayo wanda shine jagoran jam'iyyar a yankin ya ce a al'adance, arewa ta tsakiya mallakin PDP ne kuma za su kwato sa a ranar Asabar.

A wata hira da ya yi da jaridar Leadership a garin Lafiya, jihar Nasarawa, a ranar Litinin, 20 ga watan Fabrairu, Elayo ya ce:

"Saboda haka, ina hango haske ga PDP a jihohin arewa ta tsakiya a wannan zaben mai zuwa."

Ina nan a PDP ba zan koma APC ba, Gwamna Wike

A wani labari na daban, gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike ya bayyana cewa yana nan daram dam a PDP cewa karya ne baya shirin komawa APC kamar yadda ake ta hasashe.

Kara karanta wannan

Yan Kwanaki Kafin Zabe: PDP Ta Hadu Da Gagarumin Cikas a Kano, Tsagin Shehu Sagagi Sun Yi Maja Da Jam’iyyar Kwankwaso

Da yake magana a ranar Litinin, 20 ga watan Fabrairu, Wike ya ce shakka babu halin dattako na jam'iyyar APC ya matukar burge shi domin sun tsaya tsayin daka a kan mulkin karba-karba.

A cewarsa gwamnonin jam'iyyar mai mulki sun jajirce sai da aka mika tikitin shugaban kasa ga yankin kudu kamar yadda suka yi yarjejeniya tun daga farko.

Asali: Legit.ng

Online view pixel