Shi Kadai Ya San Abin da Ya Hango, Gwamnan APC Ya Fadi Wanene Magajin Buhari
- Rotimi Akeredolu ya halarci taron yakin neman zaben da APC ta shirya a mazabar tsakiyar Ondo
- Gwamnan na jihar Ondo ya yi ikirarin Bola Tinubu ne zai lashe zaben shugaban kasa da za ayi
- Akeredolu ya fadawa mutanensa su yi APC sak, ya ce ba su bukatar zaben wani ‘dan takara dabam
Ondo - Gwamna Rotimi Akeredolu ya tabbatarwa mutanen jiharsa cewa ba kowa ba ne zai lashe zabe mai zuwa ba face Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.
Jaridar The Nation a wani rahoto da ta fitar a ranar Litinin, ta ce Mai girma Rotimi Akeredolu ya hango nasarar jam’iyyar APC mai mulki a zaben 2023.
Gwamnan na jihar Ondo ya dage wajen tallata Bola Ahmed Tinubu ga mutanensa, ya yi kira gare su da su zabi wanda zai iya magance matsalolin kasar.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/24d0dd651f4487b0.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Wani hanzari: Sirri ya fito, tsohon kakakin majalisa ya ce hadari ne a ba Tinubu ragamar Najeriya
Akeredolu ya yi jawabi a wajen wani gangamin yakin neman zaben ‘dan takaran Sanatan jihar Ondo ta tsakiya da jam’iyyar APC ta shirya garin Ondo.
APC ta yi babban taro a Ondo
Rahoton ya ce mutane da-dama sun halarci taron yakin neman takarar jam’iyyar APC, Shugaban reshen Ondo, Ade Adetimehin ya ji dadin ganin jama’a.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ganin dandazon mutanen da suka yi wa ‘dan takaransu kara, Akeredolu ya ce ya kamata hakan ya jawo su samu kuri’u masu yawa a zabe mai zuwa.
![Tinubu Tinubu](https://cdn.legit.ng/images/1120/e0686487b9a5ec74.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Akeredolu: APC Sak za ayi a 2023
Baya ga mai neman zama Sanatan, Gwamna Akeredolu ya yi kira ga ‘Yan jihar Ondo da su zabi duka ‘yan takaran da jam’iyyar APC ta tsaida a zaben 2023.
Gwamnan ya kuma mika tutoci ga masu neman kujerun majalisar tarayya da na dokoki. Ku na da labari cewa ba za ayi zaben Gwamna a jihar Ondo ba.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/5f523d5649d46055.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Bola Tinubu: Yadda Nayi Ta Lallabar Buhari, Har Aka Kara Wa’adin Canza Tsohon Kudi
Akeredolu wanda shi ne Shugaban kwamitin yakin zaben Tinubu-Shettima a jihohin Kudu maso Yamma ya ce APC tayi sa’ar samun irin Bola Tinubu a 2023.
Siyasar naka sai naka!
A rahoton Vanguard, an ji Gwamnan yana ikirarin Tinubu ne kurum ‘dan takaran kujerar shugabancin kasa da zai iya kawo gyara da cigaba a kasar nan.
Tun da har Tinubu daga yankinsu ya samu tikiti, Akeredolu ya ce babu bukatar su tafi neman wani ‘dan takaran da ya fito jihohin Sokoto ko kuwa Adamawa.
A wajen gangamin ne kuma aka sanar da cewa an samu ‘yan siyasa fiye da 350 da suka fice daga jam’iyyar hamayya ta PDP, suka tsallako zuwa APC mai-ci.
Bayanin Aliyu Sabi Abdullahi
Rahoto ya zo cewa Sanatan Arewacin jihar Neja a majalisar dattawa ya ce Muhammadu Buhari yana tare da Bola Tinubu, yana goyon bayansa.
Sanata Aliyu Sabi Abdullahi wanda ya san abubuwan da ke faruwa a jam’iyya mai-ci ya ce babu rashin jituwa tsakanin shugaban kasa da 'dan takaransu.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/9fb4dab17292909f.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Atiku Ya Ankarar da ‘Yan Najeriya, Ya Fallasa ‘Mugun Shirin’ da Tinubu Yake Kullawa
Asali: Legit.ng