Bola Tinubu da Atiku Abubakar Sun Yi Sabbin Nade-Nade a Kwamitin Yakin Neman Zabe 2023
- Manyan 'yan takarar shugaban ƙasa biyu na sahun gaba sun yi sabbin naɗe-naɗe a tawagar yakin neman zaɓensu na 2023
- Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP ya naɗa mai taimaka masa musamman yayin da Tinubu na APC ya nada kakakin kwamitin arewa ta yamma
- A cewar sanarwan naɗin guda biyu, waɗanda aka baiwa mukaman zasu kama aiki ne nan take ba ɓata lokaci
Abuja - Ɗan takarar shugaban kasa a inuwar jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar ya naɗa Mista Nath Yaduma, a matsayin mai taimaka masa na musamman a ɓangaren sadarwa.
Atiku, a wata sanarwa da kakakinsa, Paul Ibe, ya fitar ranar Laraba a Abuja, yace naɗin zai kama aiki ne nan take, kamar yadda Premium Times ta ruwaito.
![Yan takarar shugaban kasa. Yan takarar shugaban kasa.](https://cdn.legit.ng/images/1120/12c1f8e7bdc0891a.jpeg?v=1)
Asali: Twitter
Kafin yanzu da ya samu wannan muƙami a tawagar kamfen PDP, Mista Yaduma, haifaffen jihar Adamawa, ya jima a matsayin hadimin Atiku Abubakar.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/8cc72349efc3dca8.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
2023: Kwankwaso Ya Ɗebo Ruwan Dafa Kansa, Na Hannun Daman Atiku Ya Maida Masa Martani
Haka nan kuma ya rike mukamai daban-daban ciki har da mai ba da shawari na musamman kan ayyuka na musamman a zamanin mulkin tsohon shugaban ƙasa, Obasanjo.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Yaduma ya yi karatu a Makarantar Inshora, Institute of Insurance, Kent, birnin Landan da kuma City College da ke New York ta ƙasar Amurka.
Wane naɗi Bola Tinubu ya yi?
A ɗaya bangaren kuma, kwamitin kamfen Tinubu/Shettima ya naɗa Amas Anka, shugaban Talabijin ɗin Thunder Blowers a matsayin mai magana da yawun tawagar arewa ta yamma.
Tsohon ma'aikacin gidan Talabijin na gwamnatin Najeriya (NTA), Mista Anka ya samu labarin naɗinsa ne a wata sanarwa da aka fitar ranar Talata a Gusau, babban birnin jihar Zamfara.
Gwamna Bello Matawalle, Ko'odinetan kwamitin kamfen Tinubu/Shettima na arewa ta yamma ne ya sanar da naɗin a taron tawagar wanda ya gudana a Kaduna.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/1e324d268089fc82.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Wike Zai Koma Bayan Tinubu? Gaskiya Ta Fito Yayin da Gwamnan APC Ya Faɗi Wata Bukata
Bugu da ƙari, a wata sanarwa da Mista Anka ya fitar ranar Laraba, yace wannan naɗin wanda ya fara aiki nan take ya maida shi matsayin mashawarci na musamman ga Kodinetan arewa ta yamma.
A cewarsa, naɗin na ɗaya daga cikin dabaru da shirye-shirye kaddamar da fara harkokin yakin neman zaɓen shugaban ƙasa a shiyyar.
Hukumar dillancin labarai ta ƙasa (NAN) ta tattaro cewa Anka, malami ne a jami'ar gwamnatin tarayya da ke Gusau. Ya yi digiri na uku a fannin kimiyyar siyasa.
A wani labarin kuma gwamnonin kudu maso kudu na PDP sun kara zama a Bayelsa, sun yanke mara wa Atiku/Okowa baya a 2023
Duk da ba'a hangi gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike a wurin ba, gwamnonin sun ce ba zasu watsa wa jam'iyyarsu ta PDP ƙasa a ido ba a zaɓe mai zuwa.
Waɗaɓda suka halarci taron sun haɗa da Godwin Obaseki na Edo, Duoye Diri na Bayelsa, Ifeanyi Okowa na Delta da kuma Udom Emmanuel na jihar Akwa Ibom.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/83d505d58ebc78ef.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
2023: Atiku Abubakar Na Shirin Janyewa Daga Takarara Shugaban Ƙasa? Gaskiya Ta Fito
Asali: Legit.ng