2023: Jerin yan takarar shugaban kasa na APC 23 da yankin da suka fito

2023: Jerin yan takarar shugaban kasa na APC 23 da yankin da suka fito

Gabannin zaben fidda dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki, mambobin jam’iyyar da dama sun ayyana kudirinsu na son darewa babbar kujerar siyasar kasar.

Adadin wadanda ke son gaje shugaban kasa Muhammadu Buhari na karuwa a kullun, lamarin da yasa jam’iyyar ta kara wa’adin siyar da fom dinta na takara wanda farashinsa yake kan naira miliyan 100.

2023: Jerin yan takarar shugaban kasa na APC 23 da yankin da suka fito
2023: Jerin yan takarar shugaban kasa na APC 23 da yankin da suka fito Hoto: @Official_ABAT, @ProfOsinbajo, @realRochas, @OUKtweets, @ChibuikeAmaechi
Asali: Twitter

Zuwa yanzu, wasu yan takara sun rigada sun siya fom dinsu.

Ga jerin wadanda suka ayyana kudirinsu na son mallakar tikitin shugaban kasa na APC:

Kudu maso Yamma

1. Asiwaju Bola Ahmed Tinubu

Kara karanta wannan

Kano: Shugaban Ma'aikatan Fadar Ganduje, Shugaban Karamar Hukuma, Ƴan Majalisa 2, Auditan APC Da Shugaban Matasa Duk Sun Koma NNPP

2. Fasto Tunde Bakare

3. Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo

4. Gwamna Kayode Fayemi na jihar Ekiti

5. Tsohon kakakin majalisar wakilai Dimeji Bankole

6. Mataimakin shugaban masu rinjaye a majalisar dattawa, Ajayi Boroffice

7. Sanata Ibikunle Amosun

Kudu maso Gabas

1. Gwamna David Umahi na jihar Ebonyi

2. Sanata Orji Uzor Kalu

3. Sanata Rochas Okorocha

4. Ministan kwadago Chris Ngige

5. Karamin ministan ilimi Chukwuemeka Nwajiuba

6. Tsohon shugaban majalisar dattawa Ken Nnamani

7. Ministan kimiyya da fasaha Ogbonnaya Onu

8. Uju Ohanenye (mace)

Kudu maso Kudu

1. Gwamna Ben Ayade na jihar Cross River

2. Tsohon shugaban jam'iyyar APC na kasa Adams Oshiomhole

3. Ministan harkokin Neja Delta Godswill Akpabio

4. Fasto Nicholas Felix

5. Ministan sufuri Rotimi Amaechi

Arewa ta tsakiya

1. Gwamna Yahaya Bello na jihar Kogi

Kara karanta wannan

Kwankwaso da wasu manyan jiga-jigan APC sun dira filin Malam Aminu Kano

Arewa maso yamma

1. Toshon gwamnan jihar Zamfara Ahmed Yerima

2. Gwamna Muhammad Badaru Abubakar na jihar Jigawa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng