Gwamnati Ta Saki Sunayen Mutane 48 da Ke Daukar Nauyin Ta'addanci a Najeriya

Gwamnati Ta Saki Sunayen Mutane 48 da Ke Daukar Nauyin Ta'addanci a Najeriya

  • Gwamnatin Tarayya ta sabunta jerin sunayen mutane da ƙungiyoyi 48 da aka ayyana a matsayin wadanda ke daukar nauyin ayyukan ta'addanci
  • An dauki wannan matakin ne da nufin toshe hanyoyin samun kuɗaɗe, kadarori, da duk wani tallafi da ke taimaka wa masu tada ƙayar baya
  • Jerin sunayen ya haɗa da fitattun ƙungiyoyi irin su ISWAP, Ansaru, da IPOB, tare da mutane irin su Tukur Mamu, Fatima Ishaq da sauran su

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Abuja – Gwamnatin Tarayya ta fitar da sabon jerin sunayen ƴan Najeriya da ƙungiyoyin da aka sanyawa takunkumi saboda zargin su da tallafa wa ayyukan ta'addanci a shekarar 2026.

Gwamnati ta dauki wannan mataki ne a ƙoƙarin da take yi na tarwatsa hanyoyin samar da kuɗaɗe ga masu tayar da ƙayar baya domin ƙarfafa tsaron ƙasa.

Kara karanta wannan

Iran ta dauki wani mataki da ya sa ta shiga gaban Amurka a shirin zaman sulhu a Pakistan

Gwamnatin tarayya ta saki sunayen mutane da kungiyoyin da ke daukar nauyin ta'addanci
Nuhu Ribadu, mai ba shugaban kasa shawara kan tsaro (hagu), da Tukur Mamu, wanda ake zargi da talla wa 'yan ta'adda. Hoto: @desert_herald, @NuhuRibadu
Source: Twitter

Jerin mutanen da ke daukar nauyin ta'addanci

Hukumar da ke sanya takunkumi ta ƙasa (NSC), wadda ke ƙarƙashin jagorancin babban lauyan gwamnati kuma Ministan Shari'a, ita ce ta fitar da jerin sunayen a shafinta na intanet.

Ga jerin sunayen mutane da ƙungiyoyin kamar yadda hukumar NigSac ta wallafa su:

  1. Abdulsamat Ohida
  2. Mohammed Sani
  3. Abdurrahaman Abdurrahaman
  4. Fatima Ishaq
  5. Tukur Mamu
  6. Yusuf Ghazali
  7. Muhammad Sani
  8. Abubakar Muhammad
  9. Sallamudeen Hassan
  10. Adamu Ishak
  11. Hassana Isah
  12. Abdulkareem Musa
  13. Umar Abdullahi
  14. Abdurrahaman Ado
  15. Bashir Yusuf
  16. Ibrahim Alhassan
  17. Muhammad Isah
  18. Salihu Adamu
  19. Surajo Mohammad
  20. Fannami Bukar
  21. Muhammed Musa
  22. Sahabi Ismail
  23. Mohammed Buba
  24. Adamu Hassan
  25. Hassan Mohammed
  26. Usman Abubakar
  27. Kubara Salawu
  28. Rabiu Suleiman
  29. Simon Njoku
  30. Godstime Iyare
  31. Francis Mmaduabuchi
  32. John Onwumere
  33. Chikwuka Eze
  34. Edwin Chukwuedo
  35. Chiwendu Owoh
  36. Ginika Orji
  37. Awo Uchechukwu
  38. Mercy Ali
  39. Ohagwu Juliana
  40. Eze Okpoto
  41. Nwaobi Chimezie
  42. Ogumu Kewe
  43. Jama'atu Wal-Jihad
  44. Ansarul Sudan (Ansaru)
  45. Islamic Province (Iswap)
  46. Indigenous Biafra (Ipob)
  47. Yan Group
  48. Yan Group Nlbdg

Kara karanta wannan

Da gaske an kai hari Abuja bayan gargadin Amurka? Gaskiya ta fito

Sojojin Najeriya suna ci gaba da kakkabe 'yan ta'adda da masu tallafa masu.
Dakarun sojojin Najeriya a bakin aikin kakkabe 'yan ta'adda da masu tallafa masu. Hoto: @ZagazOlaMakama
Source: Twitter

Muhimmancin wannan mataki ga tsaron kasa

Wannan mataki ya yi daidai da dokar hana ta'addanci ta shekarar 2022. Babban burin gwamnati shi ne tabbatar da cewa ba a bar masu tallafa wa ta'addanci su yi amfani da tsarin hada-hadar kuɗi na duniya wajen janyo rashin zaman lafiya a ƙasar ba, cewar rahoton da aka wallafa a shafin cibiyar PLAC.

Gwamnatin Najeriya, a matsayinta na mamba a Majalisar Ɗinkin Duniya, ta jaddada aniyarta na bin dukkan matakan diflomasiyya da na shari'a domin toshe hanyoyin da ƴan ta'adda ke bi wajen siyan makamai da gudanar da ayyukan da ke barazana ga rayukan ƴan ƙasa.

Wannan bincike zai shafi dukkan mutane da ƙungiyoyin da aka tabbatar suna da hannu a ayyukan ta'addanci ba tare da nuna bambanci ba.

Mutane 16 masu tallafawa 'yan ta'adda

Tun da fari, mun ruwaito cewa, gwamnatin Najeriya ta ayyana Simon Ekpa, kungiyar Lakurawa da wasu mutum 14 a matsayin masu daukar nauyin ta’addanci.

Kara karanta wannan

Wahalar da na sha a APC ko shugaban jam'iyya bai sha ba in ji Diyar Buba Galadima

An bukaci bankuna da cibiyoyin kasuwanci su toshe duk wasu kudi ko kadarori da ke da alaka da mutanen da aka bayyana a jerin.

Sunayen da aka fitar sun hada da Ekpa, Godstime Promise Iyare, da wasu kamfanoni kamar Igwe Ka Ala Enterprises da Seficuvi Global.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com