Majalisa Ta Yarda Tinubu Ya Kashe N140bn, za a Yi Aiki a Abuja da Jihohin Arewa 6

Majalisa Ta Yarda Tinubu Ya Kashe N140bn, za a Yi Aiki a Abuja da Jihohin Arewa 6

  • Majalisar dattawa ta amince gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta kashe Naira biliyan 140 matsayin kasafin hukumar NCDC
  • NCDC ce ke kula da raya shiyyar Arewa ta Tsakiya, wacce ta kunshi Abuja da jihohin Benue, Kogi, Kwara, Nasarawa, Niger, Plateau
  • Shugaba Bola Tinubu ya warewa NCDC kasafin Naira biliyan 140 a 2025 don gudanar da manyan ayyuka da na yau da kullum

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Gwamnatin tarayya za ta kashe Naira biliyan 140 na kasafin kudin hukumar raya shiyyar Arewa ta Tsakiya (NCDC) na 2025.

Kwamitin majalisar dattawa da ke kula da hukumar NCDC ne ya amince da kasafin kudin hukumar na 2025 da ya kai Naira biliyan 140.

Majalisar dattawa ta amince da kasafin hukumar raya shiyyar Arewa ta Tsakiya na N140bn
Shugabannin majalisar tarayya da kusoshin gwamnati suna kallon Shugaba Bola Tinubu ya sanya hannu kan wasu takardu. Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Majalisa ta amincewa NCDC kasafin N140bn

Amincewa da kasafin kudin ya biyo bayan zama da Tsenyil Yiltsen, shugaban NCDC, inda ya kare kasafin a gaban kwamitin a ranar Talata, inji rahoton The Cable.

Kara karanta wannan

Abubuwa 4 da ya kamata jam'iyyar ADC ta yi don kayar da Tinubu, APC a zaben 2027

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanata Titus Zam, shugaban kwamitin ya ce majalisar dattawa ta amince da kasafin ne bayan kyayyawan nazari da kuma bayanan da shugaban NCDC ya yi.

"Bayan nazari mai kyau kan abubuwan da ke kunshe a kasafin da kuma yadda shugaban hukumar da tawagarsa suka gabatar da jawabai, kwamitin ya amince da kasafin Naira biliyan 140 ga hukumar."

- Sanata Titus Zam.

A yayin gabatar da jawabi, Tsenyil Yiltsen ya ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ce ta ware Naira biliyan 140 matsayin kasafin NCDC na shekarar 2025.

Ayyukan da NCDC za ta yi da N140bn

Ya ce za a yi amfani da Naira biliyan 100 wajen gudanar da manyan ayyuka a babban birnin tarayya Abuja da kuma jihohi shida na Arewa ta Tsakiya.

Hazalika, za a yi amfani da Naira biliyan 40 wajen gudanar da ayyukan yau da kullum, da suka hada da kudin gudanar da ayyuka da kula da ma'aikata.

Kara karanta wannan

Rubutu kan Tinubu ya jawo an maka tsohon 'dan takarar shugaban kasa a kotun Abuja

This Day ta rahoto Tsenyil Yiltsen ya bayyana cewa ba wai za a kashe wadannan biliyoyin kudin ga aiki guda daya kawai ba, illa dai za a yi ayyuka masu yawa a shiyyar.

"Muna da bangarori takwas a bangaren ci gaban Arewa ta Tsakiya da suka hada da tsaro, noma, hakar ma'adanai, ci gaban yanki, ilimi, kiwon lafiya da tituna."

- Tsenyil Yiltsen.

Kwamitin majalisar dattawa ya amince da kasafin NCDC na N140bn
Shugaban kwamitin hukumar NCDC na majalisar dattawa, Titus Zam na jawabi a Abuja. Hoto: Sen Dr Titus T. Zam
Source: Facebook

Za a dauki sababbin ma'aikata a NCDC

Shugaban NCDC ya tabbatarwa kwamitin majalisar cewa za a gudanar da wadannan ayyuka ne dai dai wadaida tsakanin jihohi shida da Abuja.

"Za mu fita mu yi binciken ayyukan da kowace jiha take bukata, kuma za mu raba ayyukan ne bisa adalci tsakanin Abuja da jihohin shiyyar shida," inji Tsenyil Yiltsen.

Shugaban NCDC ya kuma yi nuni da cewa za a yi amfani da wani bangare na Naira biliyan 40 don ayyukan yau da kullum kamar biyan albashin akalla ma'aikata 200 da kuma daukar sababbin ma'aikata.

Tinubu ya sanya hannu kan dokar NCDC

Tun da fari, mun ruwaito cewa, Shugaba Bola Tinubu ya rattaba hannu kan sabuwar dokar kafa hukumar raya shiyyar Arewa ta Tsakiya (NCDC.

Kara karanta wannan

"A tsage biri har wutsiya": Lauya ya nemi bayani a kan kudin da Remi Tinubu ta tara

Ana sa ran dokar kafa NCDC za ta taimaka wajen bunƙasa tattalin arziki da samar da ayyukan ci gaba a Abuja da jihohi shida na Arewa ta Tsakiya.

Baya ga dokar kafa NCDC, Tinubu ya kuma amince da kafa kwalejin kimiyya a Rano (jihar Kano), da jami’ar lafiya a Tsafe (jihar Zamfara).

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com