Tashin Hankali: 'Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 a Ranar da Tinubu Ya Je Kaduna

Tashin Hankali: 'Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 a Ranar da Tinubu Ya Je Kaduna

  • Akalla mutane 15 ne suka mutu a hare-haren da aka kai Bokkos da Mangu a jihar Filato, lamarin da ya jefa mutane cikin firgici
  • Rahotanni sun ce maharan sun yi ruwan wuta cikin dare a Tangur da Manja, inda suka kutsa cikin gidaje suka kashe mutane
  • 'Yan bindigar sun kai wadannan hare-hare ne a ranar da Shugaba Bola Tinubu ya ziyarci Kaduna domin kaddamar da ayyuka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Filato - Akalla mutum 15 ne suka rasa rayukansu a daren Alhamis, 19 ga Yuni, 2025, yayin da 'yan bindiga suka kai mummunan hari a Bokkos da Mangu na jihar Filato.

Rahotanni sun nuna cewa maharan sun kai farmaki kauyen Manja da ke Chakfem a Mangu, da kuma kauyen Tangur a Bokkos, lamarin da ya jefa mazauna yankunan cikin firgici.

Kara karanta wannan

Zamfara: 'Yan bindiga sun shammaci mutane da dare, sun dauke liman da mutum 5

'Yan bindiga sun kutsa har cikin gidaje, sun kashe mutane 15 a Filato
Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, yayin da yake alhinin halin da ake ciki a jihar. Hoto: @CalebMutfwang
Source: Facebook

'Yan bindiga sun kashe mutum 15 a Filato

Wani rahoton Daily Trust ya ce 'yan bindigar sun shiga kauyen Tangur da misalin ƙarfe 9:00 na dare lokacin da mutane ke shirin kwanciya, yayin da harin Chakfem ya faru tun da rana.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Majiyoyi sun tabbatar da cewa maharan sun yi ruwan wuta ba kakkautawa tare da kutsa wa cikin gidaje suna kashe mutane.

A Mangu, mutane bakwai aka kashe, yayin da a Bokkos kuwa aka hallaka takwas, lamarin da ya jefa mutanen wadannan garuruwa cikin tsananin alhini.

An tabbatar da hare-haren 'yan bindiga a Filato

Shugaban kungiyar cigaban Mwaghavul kuma daraktan sansanin 'yan gudun hijira na Mangu, Shohotden Mathias Ibrahim, ya tabbatar da adadin waɗanda suka mutu a Mangu.

Kokarin da aka yi don jin ta bakin shugabannin al’umma a Bokkos ya ci tura, haka kuma kakakin rundunar ‘yan sandan Filato, DSP Alfred Alabo, bai mayar da martanin sakonnin da aka aika masa ba har zuwa safiyar Juma’a.

Kara karanta wannan

Sulhu ya jawo matsala, ƴan bindiga sun kashe manoma sama da 20 da wasu bayin Allah

Hare-haren na ci gaba da zama ruwan dare a jihar Filato, inda akasari ake danganta su da rikicin manoma da makiyaya kan filayen noma da albarkatu.

Rahoton Amnesty International ya nuna cewa mutane 2,630 ne suka mutu a Filato cikin shekaru biyu, yayin da aka tilasta wa 65,000 barin gidajensu.
Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang yayin da yake rarrashin daya daga cikin wadanda hare-haren 'yan bindiga ya rutsa da su. Hoto: @CalebMutfwang
Source: Facebook

An kashe mutum 2,630 a Filato - Amnesty

Tun farkon 2025, hare-haren da suka afku a Bokkos sun yi sanadin mutuwar mutum 52 tare da tilasta wa fiye da 2,000 kauracewa gidajensu.

Rahoton Amnesty International ya nuna cewa mutane 2,630 ne suka mutu a jihar cikin shekaru biyu, yayin da aka tilasta wa 65,000 barin muhallansu.

Ko da yake babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kisan na baya-bayan nan, amma galibi ana alakanta irin wadannan hare-haren da Fulani makiyaya.

Tinubu ya kaddamar da ayyuka a Kaduna

A wani labarin, mun ruwaito cewa, Shugaba Bola Tinubu ya kai ziyara a jihar Kaduna domin ƙaddamar da wasu muhimman ayyukan cigaba.

A ziyarar da kai Kaduna a ranar Alhamis, 19 ga Yuni, Shugaba Tinubu ya kaddamar da asibitin kwararru mai gado 300 da kuma cibiyar koyon sana’o’i da ke Rigachikun.

A wajen taron kaddamar da ayyukan ne, shugaban majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, ya shaida wa Tinubu cewa ba shi da wani abokin hamayya a Kaduna

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com