An Tsinci Gawar Babban Jami'in Dan Sandan Najeriya a Dakin Otel, Bayanai Sun Fito

An Tsinci Gawar Babban Jami'in Dan Sandan Najeriya a Dakin Otel, Bayanai Sun Fito

  • An gano gawar Sufeta Haruna Mohammed a dakin wani otal a Ogun, bayan shigowarsa tare da wata mace da misalin karfe 1:00 na dare
  • Manajan otal din ta tsinci gawar jami'in da safe, yayin da aka gano cewa macen da suka shigo tare ta bar dakin tun da sanyin safiya
  • Rundunar ‘yan sandan Ogun ta tabbatar da lamarin, tana mai cewa an fara bincike don kamo wace ta gudu da gano dalilin mutuwar jami’in

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Ogun - An tsinci gawar Sufeta Haruna Mohammed a dakin wani otal da ke jihar Ogun, lamarin da ya jawo jami’an tsaro suka fara gudanar da bincike.

Rahotanni sun nuna cewa Sufeta Haruna, wanda ke aiki a sashen ‘yan sanda na Ishashi, Legas, ya isa otal din Super G Royal tare da wata mace da misalin karfe 1:00 na daren Asabar.

Kara karanta wannan

'Ya aikata laifuffuka 5': An gurfanar da fitaccen mawakin Najeriya a gaban kotu

Rundunar 'yan sanda ta yi magana da aka tsinci gawar jami'inta a dakin otel
'Yan sanda za su fara bincike da aka tsinci gawar wani sufetan dan sanda a dakin otel. Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

An tsinci gawar dan sanda a otel

Manajan otal din, Deborah Adejobi, ta ga dakin a bude da misalin karfe 8:52 na safe. A ciki, ta tarar da gawarsa, amma ba a ga macen da suka shigo tare ba, inji rahoton Daily Trust.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rahoton ‘yan sanda ya nuna cewa mai otal din, Abiodun Olagunju, ya kai rahoton lamarin, yana mai cewa matar da ta gudu ta fito wurin karfe 6:00 na safe don neman ruwa.

Rahoton ya nuna cewa an dauke gawar Sufeta Haruna zuwa dakin ajiye gawa na Life Channel da ke Olambe domin adanawa da bincike.

'Yan sanda sun fara bincike

Kakakin rundunar ‘yan sanda ta Ogun, ta ce:

“A farko, abin da aka samu a cikin jakarsa shi ne kakin ‘yan sanda, don haka ba za a iya cewa jami’in dan sanda ba ne. Ba a samu katin shaidarsa ko wani abu da zai tabbatar da hakan ba.

Kara karanta wannan

Matashi ya gayyaci abokinsa gida ya masa kisan wulakanci da adda, ya sassara shi

“Amma bincike ya nuna cewa mamacin dan sanda ne mai mukamin Insfeto da ke aiki a sashen Ishashi na rundunar ‘yan sandan Lagos.
“An tuntuɓi DPO, kuma an tabbatar da gawarsa ce.”

Odutola ta bayyana cewa jami’an tsaro sun fara bincike don gano macen da ta gudu, yayin da ake ci gaba da kokarin gano hakikanin dalilin mutuwarsa.

Rundunar 'yan sanda ta yi magana da aka gano jami'inta ne ya mutu a Otel
'Yan sanda sun tabbatar da cewa jami'insu ne ya mutu a dakin otel. Hoto: @Princemoye1
Asali: Twitter

Binciken ya tabbatar da cewa Sufeta Mohammed yana aiki a sashen ‘yan sanda na Ishashi da ke a jihar Legas.

Duba labarai da suka shafi 'tsintar gawar dan sanda'

An tsinci gawar ɗan sanda, matarsa da ƴaƴansu 5 a cikin gidansu

An tsinci gawar wani jami'in dan sanda a gidansa a Abuja

An tsinci gawar dan sanda cikin 'yan bindiga da sojoji suka kashe a Filato

An tsinci gawar dan sanda a otel din Abuja

A wani labarin makamancin wannan, mun ruwaito cewa, an tsinci gawar wani jami'in dan sanda, Lawal Ibrahim a wani dakin otel da ke Abuja.

An gano cewa Lawal ya haɗu da wata budurwa Maryam Abba a shafukan sada zumunta watanni uku da suka gabata, inda suka yi sharholiya a otel din.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i.

iiq_pixel