Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano Ta Mika Kokon Bararta Wajen Shugaba Tinubu

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano Ta Mika Kokon Bararta Wajen Shugaba Tinubu

  • Gwamnatin jihar Kano ta buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya shiga tsakani kan rikicin da ke faruwa a masarautar Kano
  • Mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdulsalam Gwarzo, shi ne ya yi wannan kiran ga shugaban ƙasan domin hana jihar faɗawa cikin rikici
  • Mataimakin gwamnan ya kuma kare matakin gwamnatin jihar na dawo da Muhammadu Sanusi II kan sarautar Kano inda ya ce ta bi hanyar da ta dace

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kano - Gwamnatin jihar Kano ta yi kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya sa baki a rikicin masarautar Kano.

Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya yi wannan kiran yayin ganawa da manema labarai a gidan gwamnatin jihar ranar Litinin.

Kara karanta wannan

Rikicin masarauta: Bayan ya yi barazana, gwamnatin Kano ta ba Nuhu Ribadu hakuri

Gwamnatin Kano ta nemi dauki wajen Tinubu
Gwamnatin Kano ta bukaci Tinubu ya shiga tsakani a rikicin masarautar Kano Hoto: @KyusufAbba, @DOlusegun
Asali: Twitter

Kano: Ana so Tinubu ya sa baki

Mataimakin gwamnan ya ce shiga tsakanin na Bola Tinubu zai ceto jihar daga faɗawa cikin rikici, cewar rahoton jaridar The Nation.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Aminu Gwarzo ya ce jihar ta yi suna wajen zaman lafiya da kwanciyar hankali, duk da sarƙaƙiyar siyasar da take da ita.

Buƙatar gwamnatin Kano wajen Tinubu

Mataimakin gwamnan ya buƙaci shugaban ƙasan da ya dauki matakan da suka dace domin kaucewa ƙara ruruwar wutar rikicin.

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta bi tsarin da ya dace wajen mayar da Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II kan kujerarsa, rahoton jaridar Tribune ya tabbatar.

Aminu Gwarzo ya bayyana cewa ba a ba gwamnatin jihar wani umarnin kotu ba dangane da dakatar da naɗin Muhammadu Sanusi II.

Mataimakin gwamnan ya ce roƙon nasa na da nufin tabbatar da warware rikicin cikin lumana da kuma tabbatar da zaman lafiyar jihar.

Kara karanta wannan

Rikicin masarauta: 'Yan sanda sun bankado shirin tada tarzoma a Kano, sun yi gargadi

Rawar Tinubu wajen dawo da Sanusi II

A wani labarin kuma, kun ji cewa sabon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, bai yi katsalandan ba wajen dawo da shi kan sarautar Kano.

Sabon sarkin na Kano ya ce Tinubu ya fahimci cewa abin da yake faruwa a Kano al'amari ne na cikin gida kuma ya bijirewa duk wani matsin lamba domin ya yi katsalandan a ciki.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng

Online view pixel