“Dalilin da Yasa Muka Saki Mutane 313 da Muka Kama Bisa Zargin Ta’addanci a Borno,” Sojoji

“Dalilin da Yasa Muka Saki Mutane 313 da Muka Kama Bisa Zargin Ta’addanci a Borno,” Sojoji

  • Hukumar sojin Najeriya ta bayyana cewa ta saki mutane 313 da ta kama a jihar Borno bisa zargin ta'addanci, ta mika su ga gwamnatin jihar
  • Kakakin hedikwatar tsaro, Manjo Janar Edward Buba ya bayyana cewa an saki mutanen ne bisa umarnin babbar kotun tarayya da ke Maiduguri
  • Haka zalika, Buba ya ce dakarun soji da ke aiki a Borno da Gombe sun samu gagarumar nasara kan 'yan ta'adda a wannan mako

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Borno - Hedikwatar tsaro ta ce ta mika mutane 313 da ta kama ga gwamnatin Borno bisa umarnin babbar kotun tarayya da ke zamanta a Maiduguri.

Rundunar soji ta yi magana kan sakin mutane 313 da ta kama a Borno
Hedikwatar tsaro ta ce ta mika mutanen ga gwamnatin jihar Borno. Hoyo: @HQNigerianArmy
Asali: Twitter

Daraktan yada labarai na hedikwatar tsaro, Manjo Janar Edward Buba ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja.

Kara karanta wannan

Kisan sojoji: Rundunar Sojoji ta saki sunaye, hotunan mutum 7 da ake nema ido rufe

Ba a kama su da laifin ta'addanci ba?

Buba ya ce ana tsare da wadanda aka kaman ne bisa tuhuma, amma ba a samu wata shaida a kansu ba a lokacin da aka kammala bincike.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ma’aikatar shari’a ta tarayya ce ta gabatar da kararrakin, inda kotun ta bayar da umarnin a sake su.

"A bisa ga haka an mika su ga gwamnatin jihar Borno domin daukar mataki na gaba"

- Inji kakin rundunar sojoji

A halin da ake ciki kuma dakarun Operation Hadin Kai sun samu gagarumar nasara a kan 'yan ta'addan Boko Haram da ISWAP.

Sojoji sun ragargaji 'yan ta'adda

A wani rahoton na jaridar Vanguard, sojojin sun kashe 'yan ta'adda da dama tare da kame abokan aikinsu a cikin wannan mako.

Kara karanta wannan

Kotu ta yi hukunci kan shari'ar mutum 313 da ake zargi da aikata ta'addanci

Buba ya ce wasu kwamandojin ‘yan ta’adda da mayaka sun mika wuya ga sojojin da ke gudanar da aiki a kananan hukumomin jihar Borno da Adamawa.

A cewarsa, rundunar sojin sama ta Operation Hadin Kai ta kai wasu hare-hare ta sama kan ‘yan ta’adda a Arina Woje da Tumbum Shitu kusa da tafkin Chadi a ranakun 22 da 24 ga watan Maris.

'Yan ta'adda sun kashe jami'an tsaron Borno

A wani labarin, Legit Hausa ta ruwaito cewa mayakan Boko Haram sun yi wa wasu sojoji da jami'an tsaro kwantan ɓauna a jihar Borno.

Rahotanni sun bayyana cewa a yayin arangamar, an kashe soja daya da jami'an tsaro biyu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel