“Cikar Buri”: Budurwa Ta Siya Katafaren Gida Tana da Shekaru 26, Ta Baje Kolin Cikin Gidan a Bidiyo
- Wata matashiyar budurwa a TikTok ta yi nasarar siyawa kanta gida, sannan ta yada wani bidiyo a soshiyal midiya domin murnar gagarumar nasarar da ta samu
- Matashiyar, Cyndi, ta bayyana a bidiyon cewa ta siya hadadden gidan ne tana da shekaru 26 kacal a duniya
- Haka kuma, matashiyar budurwar ta nanata cewar da guminta ta siya gidan ba wai wani ne ya siya mata ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amura
Wata matashiyar budurwa ta zama mai gidan kanta a yanzu, kuma ta garzaya dandalin soshiyal midiya don yin murnar wannan babbar nasara.
Matashiyar mai suna Cyndi a TikTok, ta wallafa wani bidiyo don sanar da mabiyanta cewa ta yi nasarar mallakar katafaren gida.

Asali: TikTok
Abin da ya fi komai ban sha'awa shine ta siya gidan ne tana 'yar matashiyar budurwa, sannan ta biya da kudin aljihunta.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Cyndi ta bayyana cewa shekarunta 26 kacal a duniya, wanda hakan ya sanya ta zama mai gidan kanta a ganiyar kuruciya.
Ta rubuta:
"Yanzun nan ka siya gidan da kake mafarki da kudinta a shekaru 26. Da ikon Allah ne kawai."
Kalli bidiyon a kasa:
Martanin jama'a yayin da budurwa ta siya gida
@stargirl101 ta ce:
"Abun burgewa. Shin a Landan gidan nan yake?"
@TIEYA-MAI ta yi martani:
"Na taya ki murna!! Yi bayani ta yaya don Allah."
@NIKKIE ta yi martani:
'"Kada ki ji kunya. Fada mana wani aiki ya kamata mu yi muma."
@ORLANE KRYSTINA ta ce:
"Na taya ki murna, wannan babban cikar buri ne!!"
@nnequinn ta ce:
"Zan siya gidana na farko ina da shekaru 26. Amin."

Kara karanta wannan
Kungiyar Fulani ta Miyetti Allah ta nemi a kame dan fafutukar raba Najeriya gida biyu
Budurwa ta saki hoton gidan miliyan 1.5
A wani labarin, wata matashiyar budurwa yar Najeriya ta wallafa hotunan wani katafaren gida a Twitter sannan ta ce kudin da za a siyar da shi naira miliyan 1.5.
Matashiyar, @shalomdfirst, ta haddasa cece-kuce da wannan ikirari nata, yayin da mutane da dama suka ki yarda da maganarta.
An kammala ginin gidan tsaf, kuma ta ce naira miliyan 1.5 ake so a siyar da shi, wanda mutane suka ce ya yi arha fiye da kima.
Asali: Legit.ng