EFCC Ta Gano Kungiyar Addini Da Ke Taimakon ‘Yan Ta’adda
- Ola Olukoyede ya ce akwai kungiyoyi da shugabannin addini dumu-dumu a harkar satar kudin jama’a
- Shugaban hukumar EFCC ya tona asirin yadda ake amfani da sunan addini domin a wawuri dukiyar haram
- Olukoyede ya yi bayanin nan ne da aka gayyato shi domin yin jawabi a wani taro da aka shirya a Abuja
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.
Abuja - Shugaban EFCC mai yaki da rashin gaskiya, Ola Olukoyede ya shaida cewa hukumarsa ta bankado asirin wata kungiyar addini.
A ranar Larabar nan, Punch ta rahoto Ola Olukoyede yana cewa sun gano kungiyar addinin da ke yi wa ‘yan ta’adda safarar kudi a Najeriya.
![EFCC. EFCC.](https://cdn.legit.ng/images/1120/6d299b683b622891.jpeg?v=1)
Asali: UGC
EFCC ta tona alakar 'yan ta'adda da masu addini
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/ef50d59c06d83862.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Abin Da Yasa Kano, Jigawa Ba Su Fama Da Matsalar 'Yan Bindiga: Shehu Sani Ya Magantu
Baya ga masu taimakawa miyagu wajen yawo da kudi, EFCC ta ce akwai kungiyar addinin da aka samu da bada kariya ga marasa gaskiya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Binciken hukumar ya kai ga wasu kudi da ake zargin sato su aka yi, ko da bincike ya yi zurfi sai aka samu kudin a asusun kungiyar addinin.
Hukumar EFCC tayi taro a Abuja
Bayanan nan sun fito ne a lokacin da Olukayode ya gabatar da jawabi a cibiyar Shehu Yar’Adua wajen wani taron kwana guda da aka shirya.
Taken taron da aka shirya a garin Abuja shi ne matasa, addini da yaki da rashin gaskiya. Labarin nan ya zo a rahoton jaridar The Nation.
Olukayode ya ce an hana EFCC aiki
Ko da hukumar ta EFCC ta dage domin yin bincike a kan lamarin, sai aka aiko mata takarda inda aka umarci ta dakatar da wannan aiki.
A nan shugaban hukumar ya fasa kwan yadda aka rika samun kungiyoyi, malamai, bangarori da cibiyoyin addinai da laifin satar dukiya.
"An samu wata kungiyar addini a kasar nan tana safarar kudi domin ‘yan ta’adda."
"Mun iya gano wasu kudin sata a kungiyoyin addini, kuma da muka tuntubi kungiyoyin addinan game da lamarin, muna bincike, sai ga umarnin dakatar mu daga gudanar da aikinmu."
- Olu Olukayode
'Yan siyasa masu addinin karya
Ana da labari Buba Galadima ya ce a siyasa, sun san na-kirki, bara-gurbi, na banza da manufukai masu ci da addini domin samun matsayi.
Injiniya Buba Galadima yake cewa yanzu masu kururuwan tikitin Muslim-Muslim a zaben 2023 ba su tsira da komai a gwamnatin APC ba
Asali: Legit.ng