Murna Yayin da Shugaba Tinubu Ya Ƙara Yin Muhimman Naɗe-Naɗe Guda Biyu
- Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗa manyan sakatarori biyu a ma'aikatun gwamnatin tarayya
- Tinubu, a wata sanarwa da fadar shugaban ƙasa ta fitar, ya naɗa mutanen ne a ma'aikatar kudi da ma'aikatar albarkatun man fetur
- Wannan na zuwa ne jim kaɗan bayan shugaban ƙasar ya rantsar da manyan sakatarori takwas a fadarsa da ke birnin Abuja ranar Litinin
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
FCT Abuja - Shugaban Ƙasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da naɗin sabbin manyan sakatarori biyu a ma'aikatun gwamnatin tarayya.
Shugaban ƙasar ya naɗa manyan sakatarorin ne a ma'aikatar kuɗi da ma'aikatan albarkarun man fetur ta ƙasa, kamar yadda The Nation ta ruwaito.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/9ed2824636515a9d.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Yanzun nan: Shugaba Tinubu ya sake naɗa shugaban kamfanin man fetur na ƙasa da wasu mutum 8
![Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu. Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.](https://cdn.legit.ng/images/1120/a8e4b50489c70e4e.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Waɗan nan sabbin naɗe-naɗe biyu masu muhimmanci na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Ajuri Ngelale, ya fitar ranar Litinin, 27 ga watan Nuwamba, 2023.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sanarwan ta bayyana cewa Shugaba Tinubu ya amince da naɗin Okokon Ekanem Udo a matsayin babban sakataren ma'aikatar kuɗi ta tarayya.
Yayin da a ɗaya ɓangaren kuma Bola Tinubu ya naɗa Ambasada Gabriel Aduda a matsayin babban sakataren ma'aikatar albarkatun man fetur.
Sanarwan ta ce:
"Shugaban ƙasa Tinubu ya amince da naɗin manyan sakatarori biyu, Mista Okokon Ekanem Udo a matsayin babban sakataren ma'aikatar kuɗi da Gabriel Aduda a matsayin babban sakataren ma'aikatan albarkatun mai."
Wannan na zuwa ne awanni bayan shugaban ya rantsar da sabbin manyan sakatarori takwas da ya naɗa a baya-bayan nan.
Tinubu ya ba su rantsuwar kama aiki ne jim kaɗan gabanin fara taron majalisar zartarwa ta ƙasa (FEC) wanda ya samu halartar mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/944d82997b777b4b.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Kotun Daukaka Kara ta raba gardama, ta yanke hukunci kan zaɓen gwamnan jihar Sakkwato
Kotun Daukaka Kara Ta Raba Gardama a Shari'ar Zaben Sokoto
A wani labarin na daban Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da nasarar Gwamna Ahmed Aliyu na jihar Sakkwato a zaben watan Maris, 2023.
Kwamitin alƙalan kotun ya ce hukuncin da kotun sauraron ƙararrakin zabe ta yanke na korar karar PDP da ɗan takararta ya yi daidai.
Asali: Legit.ng