Obasanjo Ya Fusata, Ya Dauki Mataki Mai Tsauri Kan Matarsa Da Ta Ba Sarakuna Hakuri

Obasanjo Ya Fusata, Ya Dauki Mataki Mai Tsauri Kan Matarsa Da Ta Ba Sarakuna Hakuri

  • Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya bayyana wata Taiwo Obasanjo wacce ta yi ikirarin ita matarsa ce tare da ba da hakuri a madadinsa a matsayin sojar gona
  • Wata sanarwa daga ofishin tsohon shugaban kasar ta ce Taiwo Obasanjo ta dai haifa ma Obasanjo yara biyu ne, amma ba matarsa bace
  • A cewar sanarwar, babu wanda ya isa ya yi magana da yawun iyalan Obasanjo sai wadanda aka ba izinin yin hakan

Abeokuta, Ogun - Olusegun Obasanjo, tsohon shugaban kasar Najeriya, ya karyata wata Taiwo Obasanjo, wacce ta yi ikirarin cewa ita matar tsohon janar din ce tare da bayar da hakuri a madadinsa kan abun da ya yi wa sarakunan Yarbawa a jihar Oyo.

PM News ta rahoto cewa sojar gonar ta yi kira ga sarakunan da su yafewa tsohon shugaban kasar kan sawa da ya yi suka tashi tsaye da zama kamar wasu yaran makarantar firamare a wajen wani taro a jihar Oyo.

Kara karanta wannan

Wike Ya Rusa Shahararriyar Kasuwar Kilishi a Abuja, Ya Fadi Dalili

Olusegun Obasanjo ya nesanta kansa da matarsa
Obasanjo Ya Fusata, Ya Dauki Mataki Mai Tsauri Kan Matarsa Da Ta Ba Sarakuna Hakuri Hoto: Olusegun Obasanjo
Asali: Twitter

Matar Obasanjo ta ba da hakuri a madadin tsohon shugaban kasar

A wani jawabin neman yafiya, Misis Taiwo ta bukaci yan Najeriya da mutanen duniya da su yafewa mijinta.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Sai dai kuma a ranar Litinin, 18 ga watan Satumba, tsohon shugaban kasar ya ce an ja hankalinsa zuwa ga wata sanarwa daga matarsa, yana mai cewa an hada hotonsa ne da na wata Misis Taiwo Martins, marubuciyar sanarwar.

Tsohon shugaban kasar ya ce:

"Don fayyace gaskiya, Ms Martins ta haifawa Obasanjo yara biyu, Jonwo da Bunmi, amma dai ba matarsa bace ko kuma wata dangin iyalin Obasanjo."

Obasanjo ya ce tsohuwar matarsa sojar gona ce

Sanarwa daga ofishin tsohon shugaban kasar ta jaddada cewa ikirarin Taiwo na cewa ita matar Obasanjo ce ba gaskiya bane kuma ana iya daukar ta a matsayin sojar gona.

Kara karanta wannan

"Ku Taimaka Ku Yafe Masa": Uwargidan Obasanjo Ta Nemi Afuwa Wajen Sarakunan Yarbawa

Ya kara da cewar babu wanda ke da ikon yin jawabi a madadin iyalin Obasanjo sai dai tsohon shugaban kasar da kansa ko wadanda aka daurawa alhakin yin haka a hukumance.

Kehinde Akinyemi, mataimaki na musamman ga tsohon shugaban kasa Obasanjo ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Litinin.

Matar Obasanjo ta ba sarakuna hakuri a madadinsa

A baya Legit Hausa ta rahoto cewa Taiwo Obasanjo, uwargidan tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo, ta roƙi afuwa a madadin mijinta, wanda ya umarci sarakunan Yarbawa da su tashi tsaye yayin wani taro a Iseyin, jihar Oyo a ranar Juma'a, 15 ga watan Satumba.

Taiwo Obasanjo ta miƙa rokonta ga ɗaukacin Yarabawa na duniya, inda ta roƙi samun yafiya ta dindindin mai ɗorewa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng