Sojoji Sun Halaka Gawurtattun Shugabannin Yan Bindiga Ado Aliero Da Dankarami A Zamfara

Sojoji Sun Halaka Gawurtattun Shugabannin Yan Bindiga Ado Aliero Da Dankarami A Zamfara

  • Rundunar sojin sama a Najeriya ta hallaka gawurtattun 'yan bindiga biyu bayan luguden wuta a jihar Zamfara
  • Gawurtattun shugabannin mayakan sun hada da Ado Aliero da kuma Dankarami da ke karamar hukumar Zurmi
  • Rundunar ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa ta bakin kakakinta, Edward Gabkwet

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Zamfara - Rundunar sojin sama ta hallaka wasu jiga-jigan 'yan bindiga yayin luguden wuta daga sama a jihar Zamfara.

Yayin luguden wutan, rundunar ta yi nasarar hallaka wasu 'yan bindigan 10 da suka addabi yankunan Arewa maso Yamma.

Sojin sama sun hallaka gawurtattun shugabannin 'yan bindiga a Zamfara
Rundunar Sojin Sama Ta Halaka Gawurtattun Shugabannin Yan Bindiga A Jihar Zamfara. Hoto: Security Digest.
Asali: UGC

Daily Trust ta bayyana sunayen 'yan bindigan da aka hallaka da Ado Aliero da Dankarami.

Yadda sojin su ka yi wa 'yan bindigan luguden wuta daga sama

A wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ce jami'ansu sun kara kaimi wurin kakkabe 'yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma.

Kara karanta wannan

Assha: Yadda 'yan Arewa suka tafka asarar N13bn saboda abin da su Tinubu suka yi a Nijar

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Cewar sanarwar:

"A kokarinta na kakkabe 'yan bindiga da ayyukansu a yankin Arewa maso Yamma, rundunar ta kara kaimi a wani samame da ta kai tsakanin 28 zuwa 29 ga watan Yuli.
"Rundunar 'Operation Hadarin Daji ta kara kaimi wurin kai hare-hare ta sama a yankin."

Hafsan rundunar ya ba da umarnin kakkabe 'yan bindiga a yankin

Sanarwar ta kara da cewa:

"A karamar hukumar Zurmi da ke jihar Zamfara, rundunar ta kashe mayaka 16 a maboyarsu da ke biyayya ga kasurgumin dan bindiga da ake kira Dankarami.
"An kai samamen ne bayan samun bayanan sirri yadda Dankarami ke addabar mutanen yankin a karamar hukumar Zurmi.
"Har ila yau, rundunar ta kai hari maboyar 'yan bindiga da ke biyayya ga Aliero a dutsen Asola da ke karamar hukumar Tsafe a jihar bayan samun bayanan sirri.

Kara karanta wannan

Kwana Daya Bayan Rushewar Masallaci, Yan Bindiga Sun Halaka Mutum 2 a Zariya, Sun Sace Wani

"Ana zargin su ne da cewa shanu a kwanakin nan a kananan hukumomin Tsafe da Faskari ta jihar Katsina."

Kakakin rundunar sojin saman, Edward Gabkwet ya fadawa 'yan jaridu cewa babban hafsan sojin sama, Air Marshal Hassan Abubakar ya umarci ci gaba da kakkabe 'yan bindigan a yankin, cewar Vanguard.

Yan Bindiga Sun Sace Mutum 13 A Wani Sabon Hari A Zamfara

A wani labarin, 'yan bindiga sun sake kai hari a jihar Zamfara tare da sace mutane uku.

'Yan bindigan yayin harin sun hallaka mutane uku a kauyen Mayanchi da ke karamar hukumar Maru a jihar.

Harin na zuwa ne bayan tsageru sun sace mata 23 da wasu ma'aikatan kananan hukumomin Maradun da Talata Mafara.

Asali: Legit.ng

Online view pixel